Aminiya:
2025-07-24@04:05:15 GMT

Kotu ta yanke wa Murja Kunya hukuncin dauri a gidan yari

Published: 29th, May 2025 GMT

Babbbar Kotun Tarayya da ke Kano ta yanke wa fitacciyar ’yar Tiktok, Murja Ibrahim wacce aka fi sani da Murja Kunya hukunicn daurin watanni shida a kurkuku.

Alƙalin kotun Mai Shari’a Simon Amobida ya kuma ba wa Murja zabin biyan tarar Naira dubu 50.

Ya ce saboda yawan mabiyanta a shafinta na Tiktok, an nada ta jakadiyar EFCC da Babban Bankin Najeriya (CBN) wajen wayar da kan mutane kan illar wulakanta Naira a dokar Najeriya.

Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Born Bashin da ake bin Najeriya zai koma tiriliyan 162

EFCC ce dai ta maka Murja a kotun, bisa zarginta da wulakanta Naira, bayan bullar wani bidiyo da ta ɗauka tana rawa tana yi wa kanta liƙi da kuɗi a otel ɗin Tahir da ke Kano.

Murja dai ta amsa laifinta, tare da roƙon kotun ta ba ta damar amfani da shafinta mai mabiya fiye da miliyan daya wajen wayar da kan mutane kan illar wulaƙanta Naira, buƙatar da kotun ta amince da ita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Murja Kunya

এছাড়াও পড়ুন:

Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa

Dakatacciyar Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta lashi takobin sake maka shugabancin Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio a gaban kotun daukaka kara bayan an hana ta shiga harabar majalisar a ranar Talata.

Cikin bacin rai, Natasha ta shaida wa ’yan jarida cewa za ta tattauna da lauyoyinta cikin gaggawa domin fara shigar da karar, tana mai cewa matakin ya saba da hukuncin kotun da ta bayar da umarnin a mayar da ita kan kujerarta.

Lamarin dai ya biyo bayan yadda jami’an tsaron da ke gadin majalisar suka tare hanya suka hana tawagar motocinta shiga majalisar, duk kuwa da umarnin kotu na mayar da ita.

HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare

Ta kuma ce hatta dakatar da itan ma da farko ba ya kan ka’ida.

A cewar ta, “Yanzu zan je na tattauna da lauyoyina domin shirin daukaka kara alabasshi kotu ta fassara mana abin da ya faru. Ni mace ce mai bin dokokin kasa.”

Sanatar ta kuma yi alla-wadai da matakin da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio ya dauka na hana ta shigar, inda ta ce hakan tamkar raina kotu ne.

Ta kuma ce, “Akpabio bai fi karfin kundin tsarin mulkin Najeriya ba. Ina so ’yan Najeriya su sani cewa ba Ofishin Shugaban Majalisar Dattawa ne ya mayar da ni Sanata ba.

“Duk da cewa ya tafi daukaka kara, hakan ba yana nufin cewa ya soke hukuncin Mai Shari’a Binta Nyako ba ne kuma hakan ba zai dakatar da ni daga kasancewa Sanata ba.

“Mutanen Kogi ta Tsakiya ne suka zabe ni kuma su nake wakilta,” in ji Natasha.

Tun da farko dai Sanatar ta yi yunkurin shiga majalisar tare da magoya bayanta amma, amma aka hanata, dole sai da ta sauka ta tafi a kafa.

An dai girke tarin jami’an tsaron da ba a saba ganin irin su ba a majalisar, inda aka ga wasu jami’an na duba motoci tare da ma takaita yawan wadanda za su ajiya ababen hawa a wajen fakin na wajen majalisar.

Akalla an ga motocin sintiri na jami’an ’yan sanda guda biyar da aka girke a muhimman wuraren shiga majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa
  • Rayuwata Na Cikin Hatsari, A Dawo Min Da Jami’an Tsarona – Natasha 
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
  • An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Maida Gidan Marayu Zuwa Cibiyar Gyaran Mata Masu Shaye
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba