More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Najeriya tana cikin ƙasashen da suka fi yawan yara a duniya, a cewar Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF).

Sai dai a cewar Hukumar ta UNICEF, kusan rabin wadannan yara suna fuskantar kalubale, kama daga cin zarafi zuwa rashin samun kulawa da dai sauran su.


Wadannan matsaloli da yara suke fuskanta dai sun dade suna ci wa masu ruwa da tsaki tuwo a kwarya.

NAJERIYA A YAU: Tasirin Dangantakar Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”

Yayin da ake bikin Ranar Yara, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kan halin da ya yara suke ciki a yau.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Asusun yara ta majalisar dinkin duniya Ranar Yara yara

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato

An shiga ruɗani a unguwar CBN Quarters da ke cikin birnin Sakkwato, inda wani ƙaramin yaro ɗan shekara huɗu mai suna Ayman Abubakar, ya ɓace, amma daga bisani aka gano gawarsa a cikin ramin sokawe.

Ana zargin wani maƙwabcin iyayen yaron da wata mata da aikata wannan ɗanyen aiki.

An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan Kano Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole

Ƙngiyoyi da ke fafutukar kare haƙƙin yara da martabar bil adama sun bayyana wannan kisa a matsayin babban cin zarafi.

A cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da suka fitar, shugaban NACTAL na ƙasa Abdulganiyu Abubakar, Usman Ahmad daga ƙungiyar kare haƙƙin yara, da Rabi’u Bello Gandi shugaban hukumar kare cin zarafin jinsi, sun yi Allah-wadai da kisan yaron.

“Kashe wannan ƙaramin yaro cin zarafi ne na keta haƙƙin ɗan Adam, kuma lamarin da ya saɓa da doka.

“Wannan mummunan abu ne da ke ƙara nuna irin haɗuran da yara ke fuskanta a cikin al’umma.”

Ƙungiyoyin sun buƙaci a gudanar da bincike don gano gaskiya tare da ɗaukar matakin hukunta duk wanda ke da hannu a kisan.

“Muna kira da a tabbatar da an yi gaskiya da adalci, a kuma hukunta waɗanda ke da hannu a kisan Ayman. Hakazalika, ya zama dole a riƙa bayyana wa jama’a irin ci gaban da ake samu a yayin bincike lokaci bayan lokaci.”

Sun jaddada buƙatar a ɗauki matakan gaggawa na kare yara daga faɗa wa hannun miyagu.

“Kare haƙƙin yaron ɗan Najeriya lamari ne da ya kamata a bai wa fifiko a ƙasa, a daina wasa da shi.”

Mahaifin Ayman, Dakta Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda lamarin ya faru.

“Na rasa ɗana ne ranar 29 ga watan Maris, bayan ya dawo daga sallar La’asar. Mun yi ta nemansa har tsawon sati bakwai ba tare da nasara ba. Daga baya sai aka gano gawarsa a cikin ramin sokawe.”

Ya roƙi al’umma su mara masa baya wajen ganin an yi wa ɗansa adalci.

Rundunar ’yan sandan jihar, tabbatar da cewa ta kama waɗanda ake zargi, kuma an fara gudanar da bincike a kansu.

Ƙungiyoyin sun yi alƙawarin ganin cewa sun bibiyu lamarin don tabbatar da gaskiya da adalci.

“Za mu tsaya tare da iyayen Ayman domin tabbatar da cewa an yi adalci. Adalci ga Ayman, adalci ne ga kowa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adam Ta MDD Ta Bukaci A Kawo Karshen Kissan Kiyashi A Gaza
  • Yahudawan Sahyoniyya Sun Shiga Masallacin Al-Aksa Tare Da Rakiyar Sojoji
  • Ranar Yara: Yaran Nijeriya Farin Ciki Za Su Yi Ko Baƙin Ciki?
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Hare-Haren HKI Kan Wata Makaranta A Gaza Ya Kashe Mutane 46 Daga Ciki Harda Yara Kanana
  • NAJERIYA A YAU: Tasirin Dangantakar Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka
  • Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato
  • Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF