HausaTv:
2025-06-01@18:43:07 GMT

Burkina Faso ta musanta zargin kisan kiyashi da ake yi a arewacin kasar

Published: 31st, May 2025 GMT

Burkina faso ta musanta labaren da ake yayatawa na aikata kisan kiyashi a arewacin kasar.

Ministan Tsaron kasra na mayar da martani ne ga labarin da aka buga a wannan Alhamis, na RFI, na kisan kiyashi da kungiyar sa kai ta kasar (VDP) ta yi a kauyukan Dori da Gorgadji.

Ministan Tsaron Burkina Faso ya ce “mummunan zarge-zarge ne kawai ake wa kasar da nufin “dagula zaman lafiyar kasar” da kuma “bata sunan” sojojin da VDP.

Ya ci gaba da yin kira ga al’ummar Burkina Faso da su yi taka-tsan-tsan game da bayanan “farfaganda” da ke da nufin haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin al’ummomin kasar.

A cikin sanarwar da ya fitar, Céletin Simporé, ya sake nanata kudurin gwamnati na “kare fararen hula da mutunta hakkin dan Adam.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Hanyar Warware Takaddamar Shirin Makamashin Nukiliyar Iran

Ministan harkokin wajen kasar Iran yayi tsokaci kan hasashe game da kusancin cimma yarjejeniyar nukiliyar da ke gudanarwa tsakanin Amurka da Iran

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Hanyar diflomasiyya tana bukatar a dage dukkan takunkumai da aka kakabawa Iran da kuma mutunta hakkin mallakar makamashin nukiliyar Iran, yana mai cewa: Hanyar cimma yarjejeniya ta ta’allaka ne ta kan teburin tattaunawa, ba ta hanyar kafafen yada labarai ba.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya fada a jiya Alhamis cewa: Kafafen yada labarai na yada jita-jita game da yarjejeniyar da ake shirin kullawa tsakanin Iran da Amurka.

Araqchi ya ci gaba da yin tsokaci a shafinsa na Twitter a dandalin Twitter, inda ya ce: “Muna shakkar cewa an kai wannan matakin.”

Ya kara da cewa: “Hanyar yarjejeniya tana bi ta kan teburin tattaunawa ne, ba ta hanyar kafafen yada labarai ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka
  • Aragchi: Shirin Nukliyar Kasar Iran Na Tafiya Kan Fahintar Rashin Amincewa Da Babakere
  • Masu Zanga Zanga A Libya Sun Bukaci Firai Ministan Kasar Ya Sauka
  • Sojoji sun cafke ɗan ta’adda sun ƙwato makamai a Filato
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Hanyar Warware Takaddamar Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza
  • Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
  • An kama mutum 41 da ake zargi da kisan DPO a Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano