HausaTv:
2025-09-18@06:41:37 GMT

Burkina Faso ta musanta zargin kisan kiyashi da ake yi a arewacin kasar

Published: 31st, May 2025 GMT

Burkina faso ta musanta labaren da ake yayatawa na aikata kisan kiyashi a arewacin kasar.

Ministan Tsaron kasra na mayar da martani ne ga labarin da aka buga a wannan Alhamis, na RFI, na kisan kiyashi da kungiyar sa kai ta kasar (VDP) ta yi a kauyukan Dori da Gorgadji.

Ministan Tsaron Burkina Faso ya ce “mummunan zarge-zarge ne kawai ake wa kasar da nufin “dagula zaman lafiyar kasar” da kuma “bata sunan” sojojin da VDP.

Ya ci gaba da yin kira ga al’ummar Burkina Faso da su yi taka-tsan-tsan game da bayanan “farfaganda” da ke da nufin haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin al’ummomin kasar.

A cikin sanarwar da ya fitar, Céletin Simporé, ya sake nanata kudurin gwamnati na “kare fararen hula da mutunta hakkin dan Adam.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

 

A yayin samamen, kakakin ‘yansandan Neja ya ce an kama mutane shida a wurin da ake hakar ma’adinan yayin da wasu kuma suka tsere.

 

Abiodun ya bayyana sunayen wadanda ake cafken da Aliyu Rabiu, Samaila Ibrahim, Sadiku Auwal, Ibrahim Babangida, Musa Adamu da Sani Hassan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar