Leadership News Hausa:
2025-05-24@21:49:35 GMT

Adadin Kuskuren Da VAR Take Tafkawa Ya Ragu A Wannan Kakar

Published: 16th, February 2025 GMT

Adadin Kuskuren Da VAR Take Tafkawa Ya Ragu A Wannan Kakar

Masu lura da gasar sun ce kwarewar na’urar wajen yanke hukunci ya karu zuwa kashi 96.4 idan aka kwatanta da kashi 95.7% a kakar da ta gabata.

“Babu wanda yake shakku kan tasirin da ko da kuskure daya wajen yanke hukunci zai yi,” in ji wani babban jami’in kwallon kafa, Tony Scholes.

Ya ci gaba da cewa “Mun san cewa kuskure daya tal zai iya cutar da kungiya.

Sakamako da kuma makin da kungiya ke samu na iya sanyawa a kori mai horarwa ko kuma dan wasa ya rasa damarsa a cikin kungiya.”Hakan ya faru ga Erin ten Hag – domin daya daga cikin kurakurai hudu da na’urar VAR ta tafka shi ne bai wa West Ham bugun fanareti a wasa na karshe da kocin ya jagoranci kungiyar Manchester United.

Haka nan wasu alkalan wasan sun fuskanci cin zarafi, inda a kwanakin nan ‘yansanda suka kaddamar da bincike kan “barazanar cin zarafi” kan alkalin wasa Michael Oliber bayan wasan da Arsenal ta yi nasara kan Wolbes da ci 1-0 a watan Janairu. Kuma wannan ya biyo bayan matakin da alkalin wasan ya dauka na bai wa dan wasan Arsenal, Myles Lewsi-Skelly katin kora – matakin da daga baya aka soke bayan korafin da kungiyar ta shigar.

Shi ma tsohon alkalin wasa Dabid Conte, an kore shi ne a watan Disamba bayan binciken da aka gudanar a kansa. Hukumomin gasar Premier dai ba su bayyana lokuta 9 da na’urar VAR ta ki soke wani mataki ba – kuma babu tabbas ko batun jan katin da aka bai wa Lewis-Skelly na ciki amma hukumar ta yi bayani kan kurakurai hudu da na’urar ta tafka ga manema labarai.

Kuskure hudu da VAR ta tafka

Outtara ya ‘taba kwallo da hannu’ – Bournemouth 1-1 Newcastle, 25 ga Agusta.

Abin da ya faru: Dango Outtara ya zaci cewa ya ci wa kungiyarsa Bournemouth kwallon da za ta ba ta nasara lokacin da ya zura kwallon da kai. Lafari Dabid Coote ya bayar da kwallon.

Matakin VAR: Mai kula da na’urar VAR a wasan, Tim Robinson ya bai wa Coote shawarar soke kwallon, inda ya ce an taba kwallon da hannu. Kasancewar yana da yakini kan hukuncinsa, bai bukaci lafari ya kalli bidiyon lamarin ba.

Sakamako: Kasancewar babu cikakkiyar hujjar da za ta tabbatar da cewa kwallon tabbas ta taba hannun Ouattara, shugaban hukumar lura da alkalan wasan gasar Premier, Howard Webb a lokacin da ya tattauna da kafar yada labarai ta Sky Sports, ya ce – VAR ta yi kuskure wajen soke cin kwallon.

 

De Ligt ya kwashe Ings – West Ham 2-1 Man Utd, 27 ga Oktoba

Abin da ya faru: Xan wasan gaba na West Ham, Danny Ings ya fadi a cikin yadi na 18 lokacin da yake fafutikar buga kwallo tsakaninsa da mai tsaron baya na Manchester United, Mathijs de Ligt. Lafari Dabid Coote ya bayar da damar a ci gaba da wasa amma sai mai kula da na’urar VAR, Michael Oliber ya bukaci a sake dubawa a talabijin na gefen fagen wasa.

Matakin VAR: Daga nan ne Coote ya bayar da bugun fanareti, wanda dan wasa Jarrod Bowen ya zura a raga, kuma hakan ya bai wa West Ham nasara a wasan.

Sakamako: Washegari United ta sallami Ten Hag daga aiki. Daga baya Web ya ce bai kamata a bayar da fanaretin ba.

 

Jan katin da aka bai wa Norgaard – Brentford 0-0 Eberton, 23 ga Nuwamba

Abin da ya faru: Xan wasan Brentford, Christian Norgaard ya tokari mai tsaron ragar Eberton, Jordan Pickford a gwiwa lokacin da suke fafutikar kaiwa ga kwallo a cikin yadi na 18.

Mataki VAR: Alkalin wasa Chris Kabanagh bai ce an yi keta ba amma sai mai kula da na’urar VAR ya bukace shi ya sake duba wurin a talabijin din gefen fage. Bayan sake dubawa, nan take ya daga wa Norgaard jan kati.

Sakamako: Kwamiti mai zaman kansa ya soke dakatarwar da aka yi wa Norgard na wasa uku bayan korafi da kungiyar ta Brentford ta shigar.

Soke kwallon da Milenkobic ya zura – Nottingham Forest 3-2 Southampton, 19 ga Janairu.

Abin da ya faru: Nikola Milenkobic ya jefa kwallo a raga da kai inda hakan ya sanya Nottingham Forest ta yi gaba da ci 4-1.

Matakin VAR: Na’urar VAR ta umarci lafari Anthony Taylor ya soke cin saboda dan wasan Forest, Chris Wood ya yi satar fage inda hakan ya hana masu tsaron baya na

Southampton damar kalubalantar kwallon. Wood bai taba kwallon ba.

Sakamako: Kwamiti mai zaman kansa da ya duba lamarin ya ce ya kamata a bayar da cin.

Shin Ko Barcelona Ce Matsalar Dembele?

Tauraruwar dan wasa Ousmane Dembele tana ci gaba da haskawa tun bayan barinsa kungiuar kwallon kafa ta Barcelona inda ya ci gaba da saka kwazo a cin kwallaye, bayan da Paris St-Germain ta je har gida ta doke Brest 3-0 a wasan cike gurbi a Champions League ranar Talata inda Dembele ya zura kwallo biyu a raga karo na 10 yana cin kwallaye a jere a PSG, kuma na 18 jimilla a wasa 11 baya a dukkan fafatawa.

Xan wasan tawagar Faransa ya ci uku rigis a gasar zakarun Turai da Stuttgart kuma a tarihi wasu ‘‘yan wasa kadan ne da suka zura kwallo uku rigis a wasa biyu a jere a Champions League da ya hada da Lionel Messi a Barcelona a 2016 da Cristiano Ronaldo a Real Madrid a 2017.

Dembele bai samu kafa wannan tarihin ba, wanda aka sauya shi da Goncalo Ramos a minti na 82 a fafatawar. Kenan Dembele ya ci kwallo 14 a Ligue 1 da Champions League a 2025.

Tun kafin Dembele ya zura biyu a ragar Brest, Vitinha ne ya fara ci a bugun fenariti a minti na 21 da fara wasan kuma wannan shi ne wasan farko zagayen cike gurbi a sabon fasalin Champions League, za su kara a wasa na biyu a Paris ranar 19 ga watan Fabrairu. PSG, wadda ba ta taba daukar Champions League ba, an kusan fitar da ita a gasar bana a cikin rukuni, daga baya ta kara kwazo da ta doke Manchester City da Stuttgart a wasanninta na gaba.

Ana sa ran PSG za ta kai zagayen gaba cikin ruwan sanyi, wadda ake sa ran watakila ta fuskanci Liberpool ko kuma Barcelona a zagayen ‘yan 16.

 

 

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Var

এছাড়াও পড়ুন:

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

Samun Gurbin Shiga Jami’a Da Sauran Manyan Makarantu

Samun damar shiga jami’a a Nijeriya na da matukar wahala a koda-yaushe, sai ga shi wannan shekara ta 2025 ta bullo da wasu sabbin kalubale.

Daga kura-kuren da aka samu yayin yin rajista da kuma gwajin kwamfuta, don rage yawan masu shiga jami’ar, tsarin ragewar na wannan shekarar ya fi na kowace shekara.

Sama da dalibai miliyan 1.9 ne suka rubuta jarrabawar a wannan shekarar, wanda hakan yasa ta zama jarrabawa mafi girma a tarihin hukumar shirya jarrabawar.

Wannan karuwar, ta nuna karuwar yawan al’umma da kuma karuwar bukatar neman ilimi a tsakanin matasan Nijeriya. Har ila yau, wannan na nuni da cewa; adadin guraben da ake da su a jami’o’in kasar nan da sauran manyan makarantu da kwalejojin ilimi, sun yi wa daliban da ake da su kadan.

A halin yanzu, Nijeriya na da sama da jami’o’i 299 da kwalejin fasaha 150 da kuma kwalejojin ilimi da aka amince da su kusan kimanin 205.

Duk da wannan yawa nasu, guraben da aka ware na daukar dalibai, bai wuce tsakanin 500,000 zuwa 700,000 ba a duk shekara, kasa da rabin adadin wadanda suka yi rajistar jarrabawar ta JAMB.

Dalibai da dama, duk kuwa da irin cin da suka yi wa jarrabawar, amma ba su da tabbacin samun guraben shiga jami’ar, wanda hakan a karshe ke haifar da takaici da kuma damuwa.

A shekarun baya, hukumar shirya jarrabawar fagen shiga jami’a (JAMB), ta kayyade maki 140 na jami’o’i, sannan maki 100 a kwalejin fasaha da kwalejojin ilimi. Kazalika, kowace jami’a ko kwaleji akwai kwasa-kwasan da aka fi nema, suka kuma fi bai wa muhimmanci; kamar ilimin koyon likitanci (Medicine), karatun lauya (Law), ilimin Injiniya (Engineering) da kuma na Akanta (Accounting).

Makin da ake kayyadewar, yana canzawa daidai da yadda dalibai suka ci jarrabawar, guraben da ake da su na daukar daliban da kuma kwas din da ake bukata. Don haka, a duk shekarar da aka fi cin jarrabawar, dole ne manyan makarantun su kara yawan adadin makin da suke bukata, sannan kuma idan aka samu akasin haka, nan ma dole ne su sake canja adadin makin.

Haka zalika, ko da dalibi ya samu adadin makin da ake bukata na UTME, akwai yiwuwar kuma ya samu karancin makin da ake bukata na jarrabawar da jami’o’i ke shirya wa dalibai (post-UTME) ko kuma na sakamakon jarrabawar sakandire (O’Lebel).

A bana, tashin hankalin da jama’a suka shiga ya kai makura, sakamakon rahoton da suka samu na faduwa wannan jarrabawa da kuma matsalar da aka fuskanta ta na’ura. Dalibai da dama da iyaye da sauran masu ruwa da tsaki a harkar ilimi, sun nuna bacin ransu game da abin da suka bayyana a matsayin wani mummunan tsari.

Dangane da wannan abu da ya faru, Shugaban Hukumar JAMB, Farfesa Is-hak Oloyede, ya kafa kwamitin bincike. Bayan bincike na farko, hukumar ta amince da gazawar da aka samu ta fuskar gudanarwa da matsalar na’ura, wanda watakila shi ne musabbabin kawo cikas ga sakamakon jarrabawar daliban da ke Legas da kuma na wadanda ke Kudu-maso-gabas.

A kokarinta na gyara matsalar, Hukumar JAMB ta fara shirin sake jarrabawar daliban da abin ya shafa tare da alkawarin inganta sa ido da kuma gudanar da abin da ya dace.

 

Kungiyar Dalibai Kasa Ta Shawarci Dalibai Tare Da Bukatar Gyara Hukumar JAMB

Sai dai kuma a wata tattaunawa daban-daban da LEADERSHIP, Shugabannin Kungiyar Dalibai ta Kasa (NANS), sun nuna damuwarsu kan faduwa jarrabawar da daliban suka yi ba bisa laifinsu ba.

Babban Sakatare Janar na Kungiyar (NANS), Anzanku Shadrach ya bayyana cewa, dalilin wannan mummunar faduwa jarrawar da aka samu, sakamakon amfani da na’urorin zamani ne kacokan, kamar yadda ya zargi hukumar shirya jarrabawar ta JAMB da rashin gudanar da kyakkyawan shiri.

Sannan ya kara da cewa, mafi yawancin dalibai ba sa mayar da hankali kan karatunsu, yana mai jaddada cewa; kungiyarsu ta NANS, na gudanar da bincike kan wannan zargi na rashin bin ka’idoji.

A matakin wannan kungiya ta dalibai ta kasa, mun karbi korafe-korafe da dama, amma a banagaren da ake zargi ta fuskar rashin bin ka’idoji, har yanzu ba mu samu wani tabbaci ba. Don haka, mun kafa kwamitin bincike, sannan kuma mun ziyarci Shugaban Hukumar ta JAMB, domin samun bayanan sirri.

“A takaice dai, da zarar rahoton kwamitin ya nuna akwai sakaci cikin al’amarin, za mu bukaci a kori Shugaban Hukumar ta JAMB”, in ji shi.

Har wa yau, jami’in hulda da jama’a na kungiyar dalban ta kasa, Kwamared Samson Ajasa Adeyemi, ya caccaki jadawalin jarrabawar tare da yin kira da a sake duba shi.

Ya ce, sanya karfe 6:30 na safe a matsayin lokacin rubuta jarrabawar, abu ne da ba za a amince da shi ba; musamman idan aka yi la’akari da kalubalen tsaron da kasar ke fuskanta a halin yanzu.

Kazalika, ya bukaci hukumar ta JAMB da ta rungumi fasahar zamani tare da sake zamanantar da harkokikin jarrabawar, yana mai cewa; tsarin da ake da shi yanzu, na da ne wanda bai kamata a ce har yanzu da shi ake amfani ba.

 

Kalubalen Da Dalibai Suka Fuskanta

A halin da ake ciki yanzu, dalibai da dama sun fito da matsalolin da suka fuskanta yayin gudanar da wannan jarrabawa tare da yin kira wajen gaggauta yin gyara.

Olawanle Timileyin, ya bayyana cewa; tun da fari ya san cewa; wannan sakamako ba nasa ba ne, a lokacin da ya duba.

“Tunda yanzu Hukumar JAMB ta amsa laifinta, ina ganin sake tsara jarrabawar ga wadanda abin ya shafa, ba zai wadatar kadai ba, kamata ya yi hukumar ta bai wa dalibai wasu alawus-alawus, saboda kudaden da suka kashe”, in ji shi.

Wata daliba mai suna Eunice Aegh ta ce, ba a son ranta ta duba sakamakon jarrabawar ba, a cewar tata, ta samu shakku wajen tantance makin da ta samu, bayan samun labarin mummunar faduwar jarrabawar da aka samu.

“Hatta abokaina na makaranta da suka fi ni hazaka, ba su iya samun maki 200 ba,” in ji ta.

 

Jarrabawar Da Aka Sake Shiryawa

A ranar Juma’ar da ta bgabata ne aka fara gudanar da jarrabawar UTME ta shekarar 2025 da Hukumar JAMB ta shirya wa wadanda abin ya shafa a dukkanin fadin kasar nan.

Dole ne a sake shirya jarrabawar ga daliban, sakamakon matsalar da aka fuskanta ta na’ura da sauran al’amuran da suka shafi kayan aiki da suka fuskanta yayin rubuta jarrabawar.

LEADERSHIP ta rawaito cewa, an ga ana sake tantance daliban da za su sake rubuta jarrabawar ranar Juma’ar da ta gabata a cibiyoyi daban-daban, ciki har da Jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke Awka a Jihar Anambira.

An kuma samu labarin cewa, wasu daga cikin daliban sun samu sakwanni kasa da sa’o’i 24 na sake shirya jarrabawar, inda da dama suka samu damar tafiya wurare masu nisa da za su rubuta jarrabawar.

Haka zalika, iyayen wadannan dalibai sun bayyana ra’ayoyinsu daban-daban tare da fatan samun nasara wajen rubuta jarrabawar, musamman ganin abin da ya faru na rashin dadi.

Wata uwa mai suna Madam Ijioma Ugwu da ke zaune a Abuja, wadda kuma danta na daya daga cikin wadanda za su sake zana jarrabawar a Jihar Inugu a safiyar ranar Juma’a, ta koka da yadda har yanzu hukumar ta kasa magance wasu matsaloli da ke tasowa.

A cewarta, idan har hukumar ta JAMB za ta ci gaba da kasancewa a matsayinta na hukumar shirya jarrabawar share fagen shiga jami’a, ya kamata ta bunkasa ayyukanta tamkar yadda aka kafa ta a shekarar 1978.

Sannan, ta kuma koka kan yadda aka sanya wa dalibai karfe 6:30 na safe a matsayin lokacin fara rubuta jarrabawar.

Farfesa Yusif Ali Ya Jinjina Wa Oloyede Kan Amincewa Da Kuskuren Da Ya Yi

An yaba wa Shugaban Hukumar JAMB na Kasa, bisa gaskiya da karbar kuskuren da suka yi a fannin da ya shafi na’urar fasaha wajen rubuta jarrabawar wannan shekara ta 2025 a wasu sassan kasar nan.

A wata sanarwa da Farfesan ya fitar, ya yaba da gaskiya da kuma dattakon Oloyede a bangaren jagoranci, wanda kusan za a iya cewa; ba a saba da shi ba, ta yadda ya dauki cikakken alhaki da kuma nuna tausayi ga daliban da abin ya shafa.

Ya lura cewa, Oloyede ya zabi amincewa da laifukan ne maimakon yin watsi da su, kamar yadda yawancin jami’an gwamnati ke yi, kazalika ya bayyana shi a matsayin shugaba nagari, wanda ba ya fifita bukatarsa a kan ta sauran wadanda yake jagoranta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karon farko an tattauna kai tsaye tsakanin ECOWAS da AES
  • Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
  • Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon Ɗan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana
  • Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
  • Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
  • Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai
  • Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi
  •   Ma’ariv: “Isra’ila” Ta Zama Saniyar Ware A Duniya
  • Ma’aikatar Tsaro Ta Fitar da Rahoton Nasarori Karkashin Shirin “Sabuwar Fata” na Shugaba Tinubu
  • Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn