Birtaniya ta dage takunkumin da ta kakaba wa wasu manyan jami’an Zimbabwe
Published: 28th, May 2025 GMT
Gwamnatin Birtaniya ta sanar da dage takunkumin da ta kakaba wa wasu manyan jami’an gwamnatin Zimbabwe.
Birtaniya ta ce ta yi hakan ne domin kyautata dangantaka tsakanin kasashen biyu.
Ma’aikatar harkokin wajen Birtaniyar ta bayyana cewa za ta dage takunkumin da ke kan mutum hudu da kuma kamfanin kera makamai mallakar gwamnati a Zimbabwe.
Wannan matakin ya zo watanni bayan Tarayyar Turai ita ma ta sassauta nata takunkumin kan Zimbabwe.
Birtaniya ta saka takunkumin ne a lokacin saboda damuwa da abinda ta kira take hakkin dan Adam da aka rika samu a kasar ta Zimbabwe.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Birtaniya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”
Jaridar Vadiot Ahranot ta HKI ta buga labarin dake cewa; Shugaban kasar Chile Gabriel Boric ya bayar da umarni a janye jami’an diplomasiyyarsa kasarsa masu kula da alakar soja daga ofishin jakadancin kasar tasa a Tel Aviv.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Chile ta wallafa wani sako a shafinta na “Internet” cewa; Ofishin jakadancin nata ya sanar da mahukunta wannan haramtacciyar cewa sun janye jami’an diplomasiyyar biyu.
Kasar ta Chile ta bayyana dalilinta na yin haka da cewa, shi ne yanayin da mutane Gaza suke ciki ta fuskar jin kai ta tabarbarewar harkokin rayuwa saboda yakin da Isra’ila take yi. Haka nan kuma kin amincewar “Isra’ila” da a shigar da kayan agaji cikin yankin na zirin Gaza.
Ita dai kasar Chile tana cikin wadanda su ka yi ta kira ga “Isr’ila” da ta datakar da yakin da take yi a Gaza, sannan kuma ta bari a shigar da kayan agaji cikin yankin.
A bisa rahoton jaridar ta Yedioy Ahranot, kasar Chile tana da jami’an soja uku a ofishin jakadancinta da su ne na ruwa, kasa da sama, amma tun watanni biyu da su ka gabata aka janye daya daga cikinsu, yanzu kuma aka jane biyun da su ka saura.
Ana sa ran cewa a ranar Lahadi mai zuwa da shugaban kasar ta Chile za iyi jawabin shekara-shekara ga al’ummar kasar, zai sanar da yanke alakar diplomasiyya da HJKI.
A gefe daya, Falasdinawa sun yaba da matakin da kasar ta Chile ta dauka na janye jami’an diplomasiyyarta daga HKI tre da bayyana shi da cewa; mataki ne mai muhimmanci da kuma nuna jarunta domin nuna kin amincewa da laifukan da HKI take tafkawa a Falasdinu.