Leadership News Hausa:
2025-07-03@14:43:11 GMT

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

Published: 18th, May 2025 GMT

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

Wani babban jami’in hukumar jin daɗin alhazai ta babban birnin tarayya Abuja wanda ya buƙaci a sakaya sunansa ya tabbatar da cafke Yahaya Zango inda ya ce ya daɗe yana wasan ɓuya tsakaninsa da jami’an tsaro kafin dubunsa ta cika a yau.

“Ya so ya shige cikin sauran alhazai amma tuni jami’an tsaro sun gama shirya kama shi” a cewar jami’in.

Har kawo yanzu dai jami’an tsaro na farin kaya ba su ce komai ba game da kamen da suka yi.

Nigeria dai tana fama da matsalar rashin tsaro na masu garkuwa da mutane da ƴan bindiga musamman a yankin Arewa ta tsakiya da Arewa maso yamma. Duk da yunƙurin da jami’an tsaro suke yi amma har yanzu matsalar tsaron tana ciwa gwamnati tuwo a ƙwarya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jami an tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana

Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta sanar da kammala dawo da dukkan  alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana gida Najeriya daga kasar Saudiyya.

A cikin wata sanarwar da Daraktar Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta fitar ranar Laraba, ta ce jirgin karshe dauke da alhazai 88 ya bar birnin Jiddah da misalin karfe 10:30 na safe dauke da alhazan jihar Kaduna da Katsina.

Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta

A cewar hukumar, hakan ya kawo karshen jigilar da aka shafe kwana 20 ana yi tun ranar 13 ga watan Yuni.

A sakonsa na bankwana ga alhazan, shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bayyana godiyarsa ga Allah kan kammala aikin cikin nasara.

Ya kuma bukaci alhazan da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’ar Allah ya kawo mata karshen tarin matsalolin da suke addabar ta.

Farfesa Abdullahi ya kuma tunatar da su cewa Aikin Hajji ibada ce da take nuna zaman lafiya da kwanciyar hankali, sannan ya buƙace su da su ci gaba da zumuncin da suka ƙulla a tsakaninsu lokacin ibadar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3
  • Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
  • An Kashe Kusan Mutane 1500 Kan Sabanin Mazhaba A Kasar Siriya A Wata Guda
  • Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu
  • Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  •  Na’im Kassim: Mamaya Tana Da Ranar Da Za Ta Zo Karshe
  • Iran Ta Ce: Ba Za Ta Koma Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Sai A Kan Wasu Sharudda