Leadership News Hausa:
2025-06-30@22:03:36 GMT

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

Published: 30th, June 2025 GMT

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

Gabanin fara wasannin ƙasashen Afrika na ƙwallon ƙafa ta mata da hukumar ƙwallon ƙafa ta nahiyar Afirka (CAF) ta shirya a ƙasar Morocco da za a fara a ranar Asabar, Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afrika (CAF) za ta ƙaddamar da sabon kofin gasar a wani ɓangare na ƙoƙarin ɗaukaka wasan ƙwallon ƙafa na mata a nahiyar Afrika.

A ranar Laraba, 02 ga watan Yuli na shekarar 2025 za a ƙaddamar da sabon kofin gasar cin kofin Afrika ta mata a ƙasar Morocco, ƙasar da za ta karɓi baƙuncin gasar ta bana, sabon kofin wani ɓangaren ne na burin shugaban CAF Dr Patrice Motsepe na bunƙasa ƙwallon ƙafa na mata a Afrika.

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

CAF za ta ƙaddamar da kofin a shafukanta na sada zumunta sannan kuma a wani taron da ta shirya gudanarwa tare da masu ɗaukar nauyin gasar ta bana, a ranar Asabar 05 ga Yuli, 2025 za a fara gasar cin kofin Afrika ta mata, a filin wasa na Olympic da ke Rabat yayinda da masu masaukin baƙi, Morocco za ta karawa da Zambia.

Ranar Lahadi 6 ga watan Yuli Nijeriya za ta kece raini da ƙasar Tunisia a wasan rukunin B a filin wasa na Larbi Zaouli dake birnin Casablanca na ƙasar Moroko da misalin karfe 4 na yamma Agogon Nijeriya a ƙarƙashin jagorancin koci Justin Madugu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ƙwallon ƙafa

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila na neman ƙulla hulɗa da Siriya da Lebanon

Isra’ila ta bayyana shirin ƙulla hulɗa ta diflomasiyya da ƙasashen Siriya da Lebanon da suka daɗe ba sa ga maciji da juna a yankin Gabas ta Tsakiya.

Wannan na zuwa ne bayan samun lafawar rikici tsakanin Isra’ila da Iran.

Kasar Isra’ila ta ce za ta ƙulla hulɗa da ƙasashen da suka daɗe suna zaman doya da man ja, amma ta ce babu batun tattauna makomar tuddan Golan da ta ƙwace daga hannun Siriya.

Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi An sanya dokar hana fita a Kaduna

Ministan Harkokin Wajen Isra’ila, Gideon Saar wanda ya bayyana hakan a wannan Litinin din ya ce ƙasarsa tana da yaƙini kan karya lagon ƙasar Iran lokacin fito na fito na tsawon kwanaki 12 da suka yi a bayan nan.

Dangane da hakan ne Isra’ilan ke cewa za ta ƙara ƙulla hulɗa ta diflomasiyya da ƙasashen yankin.

A shekara ta 2020 Isra’ila da ƙulla hulda da kasashe da dama na Laraba na Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain gami da Maroko da ke zama karo na farko, bayan wadda Isra’ila ta ƙulla da Jordan a shekarar 1994, da kuma wadda aka fara yi da Masar a shekarar 1979.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila na neman ƙulla hulɗa da Siriya da Lebanon
  • Jana’izar Aminu Ɗantata: Abba da Sarki Sanusi sun tafi Saudiyya
  • Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
  • Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City
  • Mummunan Hatsari Ya Lashe Rayukan ‘Yan Mata 18 A Kasar Masar Dukkaninsu ‘Yan Kasa DA Shekara 21
  • Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya
  • Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya
  • Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
  • Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025