Janar Abdurrahim Musawi wanda ya tattauna ta wayar tarho ta kwamandan sojojin jamhuriyar  musulunci ta Pakistan, Asim Munir, ya yi jinjina akan mataki na jarunta da Pakistan din ta dauka akan harin da HKI ta kawo wa Iran, haka nan kuma yadda ta nuna goyon bayanta ga Iran.

Janar Musawi ya  kuma yi ishara da matsayar gwamnati da al’ummar Pakistan akan ta’addanci na HKI, kamar kuma yadda ya bayyawa kwamandan sojojin kasar ta Pakistan yadda Amurka ta taimakawa HKI a tsawon kwanaki 12 na yakin.

 Har ila yau, janar Musawi ya ce; Tare da cewa mun rasa kwamandoji masu girma a farkon harin ta’addancin, sai dai kuma duk da haka, mun hana ‘yan sahayoniyar cimma manufofinsu.

A farkon yakin dai, kasar Pakistan ta bakin shugabanninta sun yi tir da harin na HKI, tare da nuna cikakken goyon bayansu ga jamhuriyar musulunci ta Iran wacce su ka bayyana a matsayin ‘yar’uwa kuma makwabciya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Tawagogin tattauna batutuwan cinikayya da tattalin arziki na Sin da Amurka, sun kara tabbatar da bayanan tsarin aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma yayin tattaunawar da suka yi ta wayar tarho a ranar 5 ga watan nan na Yuni, da karfafa sakamakon da aka cimma a tattaunawar cinikayya da tattalin arziki da aka yi a Geneva.

Kakakin ma’aikatar kula da cinikayya na Sin ne ya bayyana haka yau, inda ya ce an tabbatar da bayanan ne bayan bangarorin biyu sun ci gaba da tuntubar juna bayan tattaunawa mai ruwa da tsaki da suka yi a birnin London a ranekun 9 da 10 ga wata.

Ya ce Sin za ta bi tsarin doka wajen sake nazari da amincewa da izinin neman fitar da wasu kayayyaki da aka takaita fitarwa, ita kuma Amurka za ta cire jerin takunkuman da ta kakabawa kasar Sin.

A cewar kakakin, Sin na fatan Amurka za ta yi amfani da tsarin tuntubar juna kan tattalin arziki da cinikayya dake tsakaninsu, ta ci gaba da karfafa fahimtar juna da rage sabanin dake akwai da karfafa hadin gwiwa don ganin dangantakar Sin da Amurka kan tattalin arziki da cinikayya ya dore cikin aminci. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka
  •  HKI:Har Yanzu Matatar Man Fetur Ta Haifa Ba Ta Koma Aiki Ba
  • Najeriya A Yau: Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya
  • Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
  • Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau 
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta da Isra’ila ta kashe
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta Isra’ila ta kashe
  •  Arakci:  Idan Aka Kai Iran Bango Za Ta Fito Da Hakikanin Karfin Da Take Da Shi
  • Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva