Jarumin Matashi Ya Ragargaji Wani Ɗan Fashi A Kano
Published: 1st, July 2025 GMT
Wani ɗan Fashi da makami ya rasa ransa bayan da yayi yunƙurin yin fashi a unguwar Dorayi Babba, Unguwar Jakada, Kano. Rahotanni sun bayyana cewa ɓarawon, wanda aka gano sunansa Musa Nuhu, ya kutsa cikin wani gida riƙe da makami, wata wuka da nufin yin fashi a wani gida.
Bayan shiga cikin gidan, ɓarawon ya kai hari kan wasu mata biyu tare da jikkata su.
Kakakin rundunar Ƴansanda ta Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa a shafinsa na Facebook. Ya bayyana cewa an yi nasarar daƙile harin ne sakamakon jarumtar da ɗaya daga cikin mazauna gidan ya nuna.
“An sami nasarar daƙile ɓarawon bayan wata fafatawa da wanda ake yunƙurin kai wa hari ya yi. An garzaya da shi asibiti domin samun kulawa, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarsa sakamakon munanan raunukan da ya samu,”
in ji sanarwar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An kama ɗan shekara 18 kan zargin fashi da makami a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta cafke wani matashi mai shekaru 18, Hassan Aminu Sadiq, bisa zargin aikata fashi da makami a lokuta daban-daban, bayan wani samame da aka kai unguwar unguwar Yelwa da ke garin Kwadon a Karamar Hukumar Yemaltu Deba.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar 9 ga Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 2:30 na rana, yana ɗauke da kunshin ganyen da ake zargin tabar wiwi ne.
An kama basarake kan zargin yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Gombe EFCC ta saki TambuwalBinciken da aka soma gudanarwa ya nuna cewa Hassan yana cikin jerin mutanen da ake nema ruwa-a-jallo, bisa zarginsa da hannu a manyan hare-hare biyu na fashi da makami da ake ci gaba da shari’arsu a Babbar Kotun Jihar Gombe.
“An kama shi ne bayan samun bayanan sirri, kuma ya amsa cewa ya shiga cikin waɗannan hare-hare biyu na fashi da makami,” in ji DSP Abdullahi.
Kwamishinan ’Yan Sanda, CP Bello Yahaya, ya ba da umarnin a mika wanda ake zargin tare da kayan laifin da aka samu ga sashen binciken manyan laifuka domin ƙarin bincike da gurfanar da shi a gaban kotu.
Rundunar ta jaddada aniyarta na kawar da miyagun laifuka a jihar tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai cikin lokaci domin taimaka wa ayyukan jami’anta.