Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
Published: 2nd, July 2025 GMT
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da cibiyar Fasaha ta Zamani ta Arewa maso Yamma da hukumar sadarwa ta ƙasa (NCC) ta gina a Kano, wadda matasa suka lalata a lokacin zanga-zangar ƙuncin rayuwa ta #EndBadGovernance a watan Agustan 2024. Ministan Harkokin Sadarwa Dr. Bosun Tijani, ne ya wakilci shugaban ƙasa a wajen bikin ƙaddamarwar.
A jawabin sa, Minista Tijani ya bayyana cewa wannan katafaren aiki da gwamnatin Tinubu ta samar ƙarƙashin shirin Renewed Hope Agenda, zai iya zama babbar hanya ga matasa su tsira daga talauci idan har suka yi amfani da damar yadda ya kamata. Ya bayyana damuwarsa kan lalata cibiyar mako guda kafin a ƙaddamar da ita, duk da cewa an kammala aikin tun watan Janairu.
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da TinubuMinistan ya ce lokacin da ya samu labarin lalata cibiyar, bai bar fushinsa ya hana shi sake ci gaba da aikinta ba. Ya tuntuɓi kamfanoni kai tsaye don a gyara cibiyar cikin gaggawa ba tare da dogon tsarin gwamnati ba. Ya kara da cewa shirin cibiyar na da burin samar da ƙwararrun matasa miliyan uku da za su samu horo a fannin fasaha, domin samun damar ci gaba da kuma shiga kasuwannin duniya.
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ta bakin mataimakinsa Abdussalam Gwarzo, ya ce jihar na da shirin horas da matasa 300,000 kan fasahar zamani nan da shekarar 2027. Ya bayyana cewa tuni aka fara horar da ma’aikatan gwamnati 5,000 da suka samu ƙwarewa a fannin fasaha. Shugaban hukumar NCC, Dr. Aminu Maida, ya ce wannan cibiya ta fasaha na daga cikin dabarun raya tattalin arziƙin dijital na ƙasa, kuma za ta taimaka matuƙa wajen haɓaka ƙwarewar matasan jihar Kano.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano
Mutum 12 sun rasu yayin da wasu biyar suka jikkata a wani hatsarin mota da ya auku a ƙauyen Samawa, da ke Ƙaramar Hukumar Garun Malam a Jihar Kano.
Hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:40 na daren ranar Juma’a a kan titin Zariya zuw Kano.
Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe An sake ceto matafiya 10 da aka sace a KogiTirela ƙirar DAF mai lambar KMC 931 ZE, wadda ke ɗauke da kaya da fasinjoji ta yi hatsarin.
Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta ce bincike ya nuna cewar matsala ce ta haddasa hatsarin.
Tirelar na ɗauke da mutum 19, wanda 12 daga cikinsu suka rasu, sai wasu biyar da suka jikkata.
Mutum biyu ne kacal suka tsallake rijiya da baya ba tare da sun ji rauni ba.
An kai waɗanda suka jikkata Babban Asibitin Garin Kura, sannan an kai gawarwakin waɗanda suka rasu Asibitin Nasarawa.
Kwamandan FRSC na Kano, M.B. Bature, ya ziyarci wajen da hatsarin ya auku, inda ya zargi lodin kaya masu yawa da rashin bin dokokin hanya da haddasa hatsarin.
Ya gargaɗi direbobi kan haɗa kaya, dabbobi da fasinjoji a mota ɗaya.
A madadin Babban Kwamandan FRSC, Dauda Ali Biu, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, tare da yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi.