Har ila yau, Maishaddar ya ci gaba da bayyana cewa; dangane da batun da mutane ke yi na cewa, alaka tsakaninsa da jarumi kuma mawaki Umar M. Sharif ta yi tsami, duba da cewa; an daina ganinsa a ci gaban shirin ‘Gidan Sarauta’ da Maishadda ke daukar nauyi, Bashir ya bayyana cewa; wannan magana ko kusa babu kamshin gaskiya a ciki, don ba a ga Umar a shirin ‘Gidan Sarauta’ zango na 4 ba, wannan ba dalili ne da zai sa a yi tunanin ko akwai wata matsala a tsakanina da shi ba, domin kuwa; a duk wani shiri mai dogon zango, akwai lokacin da za a daina ganin jarumi, amma kuma daga baya ya sake bayyana.

Bashir ya kara da cewa, yanzu kamar yadda ake daukar fim din ‘Alakata da Nana Firdausi’, har wasu ma ke tunanin ko akwai maganar aure a tsakaninmu, duk da dai Allah ne ke yi; saboda yanzu haka, matata ’yar fim ce. Don haka, zuwa yanzu dai babu wani batu na aure tsakanina da Nana, kawai dai muna da fahimtar juna tsakaninmu, sannan kuma na yi amanna da yanayin aikinta, saboda duk wani aiki da za mu yi tare da ita; ina yaba aikin nata kwarai da gaske, saboda yadda ta ke mayar da hankali wajen ganin ta yi abin da ya dace, musamman ma aikin kamfanina.

Lokacin da yake amsa tambaya a kan burin da yake da shi a wannan masana’anta, Bashir ya ce; babu wani burin da yake da shi a yanzu da ya wuce a ce watarana ya dauki nauyin fim a wata kasa daban, ba Nijeriya ba; musamman Kasar Indiya. 

“Burina yanzu a Masana’antar Kannywood, bai wuce ganin na zama ‘International Furodusa’ ba, wato ya kasance ina yin fina-finai ba a iya nan gida Nijeriya ba, har ma da kasashen duniya; musamman ma Kasar Indiya”, in ji shi.

“Domin kuwa, in dai ana iya yin fim a samu riba a Kasar Indiya, to ni ma ina fatan watarana a ce nayi, hakan ya sa tun a yanzu na fara gayyato wasu daga cikin jaruman da ba Arewacin Nijeriya suke aiki ba, kamar irin su Kanayo O. Kanayo da sauran makamantansu; domin su zo su taya ni aiki. Burin da nake da shi ga wannan masana’anta mai albarka, ba zai fadu ba; domin idan da zan samu dama, zan yi abin da zai sa Kannywood ta shiga duniya kowa da kowa ya santa”. 

Ya ci gaba da cewa, harkar fim; ba karamar harka ba ce a idon duniya, kamar yadda wasu ke tunani. Dalili kuwa shi ne, a fim ne za ka samu daukaka, kudi da kuma masoya, sannan kuma a nan ne za ka bugi kirjin cewa; an san fuskarka, haka zalika an san sunanka, har inda ba ka yi tsammani ba, kuma a harkar fim ne kadai za ka taka kafarka inda ba ka taba tsammanin cewa; za ka iya takawa ba, misali a Nijeriya, duk inda gwamna ke tunanin an san shi, haka nan dan fim ma zai yi wannan tunani, domin kuwa ta hanyar fim sunansa ya zaga ko’ina.

A karshe, Bashir Abubakar Maishadda, wanda ake yi wa lakabi da ‘King Of Bod Office’, ya yi kira ga mutane da su daina raina mutum a duk inda suka gan shi, domin kuwa ba su san abin da zai zama a nan gaba ba, har ma ya yi misali da kansa, inda ya ce a farkon lokacin da ya shigo masana’antar, mutane da dama sun sha tsangwamar sa tare da toshe wasu hanyoyin da suke tunanin zai iya koyon wani abu, amma kuma yanzu da Allah ya mayar da shi abin da ya zama, sai suke mamaki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kannywood

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza

Rahotanni sun bayyana cewa kididdigar da ma’aikatar harkokin wajen yankin falasdinu ta fitar ya nuna cewa sojojin Isra’ila sun kashe akalla yan mata 33000 a ci gaba da yakin kare dangi da take yi kan alummar Gaza.

Ma’aikatar fa fitar da wannan sanarwar ce a wajen taron ranar kawo karshen hare-hare kan mata ta duniya . kuma tayi kaca-kaca da gwamnatin sahayuniya game da irin muggan laifukan yaki da ta tafka, inda ta rika amfani da makamai na zamani kan alummar falasdinu

Kididdigar ta nuna cewa sama da mata 12500 da kuma yara 20,000 ne Isra’ila ta kashe a harin da ta kai tun daga watan oktoban shekara ta 2023.

Har ila yau ma’aikatar ta bayyana cewa lallai a kwai bukatar a dauki matakin gaggawa na matsin lamba domin kawo karshen ci gaba da mamaye yankunan falasdinawa da HKI ke yi, kuma tayi aiki da kudurin kafa kasashe guda biyu da zai bada garanti wajen kafa kasar falasdinu..

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa November 26, 2025 Sojojin Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar  Guinea Bissau November 26, 2025 Larijani Iran Tana Maraba Da Tattaunawa Ta Gaskiya Amma Ba Tsararren Sakamako Ba November 26, 2025   November 26, 2025 Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza November 26, 2025 Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe November 26, 2025 Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta November 26, 2025 Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki November 26, 2025 Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • UNIFIL: Isra’ila tana sabawa wa kudurorin MDD a cikin  Lebanon
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta