Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) ta sanar da cewa; Da akwai ‘yan kasar Sudan miliyan 4 da suke rayuwa a kasashen makwabta da suke fuskantar hatsarin yunwa.

Sanarwar hukumar ta kunshi cewa mutanen sun fice daga kasarsu ne tun asali saboda neman abinci da kuma mafaka daga yakin da ya barke a cikin Sudan tun a tsakiyar watan Aprilu na 2023.

 Bugu da kari sanarwar hukumar ta zo ne a matsayin gargadi saboda yadda ake samun koma bayan taimakon da ake amfani da shi wajen tafiyar da rayuwar ‘yan hijirar.

Har ila yau sanarwar ta ce; da dama daga cikin iyalan da suke isa kasashen makwabta, suna cikin gajiya da kuma rashin abinci mai gina jiki, haka nan kuma rashin isassun tufafi.

Da akwai kasashe 7 da suke makwabtaka da Sudan da ‘yan hijirar su ka shiga, da suke da bukatuwa da taimakon kudade da kayan abinci saboda kula da ‘yan hijirar.

Kasashen sun hada Chadi, Afirka ta Tsakiya, Masar, Habasha, sai kuma kasashen Libya, Uganda da Sudan Ta Kudu.

A halin da ake ciki a yanzu ‘yan hijirar suna cin kasa da abincin da ya kamata a ce suna samu a kowace rana, kamar yadda hukumar abininci ta duniya ta sanar.

Hukumar Abincin Ta Duniya ta kuma ce; Idan har daga nan zuwa wani lokaci ba a gabatar da taimako gare ta ba, to a cikin watanni kadan ayyukan nata za su tsaya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yan hijirar

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

Uba ya ce dakarun sun ci gaba da bincike da fatattakar ƴan ta’addan don hana su sake samun damar motsi a yankin Arewa maso Gabas.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe October 11, 2025 Tsaro Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba October 11, 2025 Tsaro Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cibiyar Lafiya Ta Nasser Ta Ce: Yaran Gaza 5,500 Suna Bukatar Agajin Gaggawa A Kasashen Waje
  • Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar.
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina
  • ’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali – Likita