‘Yan Guudun Hijirar Sudan Miliyan 4 Suna Fuskantar Yunwa A Kasashen Makwabta
Published: 1st, July 2025 GMT
Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) ta sanar da cewa; Da akwai ‘yan kasar Sudan miliyan 4 da suke rayuwa a kasashen makwabta da suke fuskantar hatsarin yunwa.
Sanarwar hukumar ta kunshi cewa mutanen sun fice daga kasarsu ne tun asali saboda neman abinci da kuma mafaka daga yakin da ya barke a cikin Sudan tun a tsakiyar watan Aprilu na 2023.
Bugu da kari sanarwar hukumar ta zo ne a matsayin gargadi saboda yadda ake samun koma bayan taimakon da ake amfani da shi wajen tafiyar da rayuwar ‘yan hijirar.
Har ila yau sanarwar ta ce; da dama daga cikin iyalan da suke isa kasashen makwabta, suna cikin gajiya da kuma rashin abinci mai gina jiki, haka nan kuma rashin isassun tufafi.
Da akwai kasashe 7 da suke makwabtaka da Sudan da ‘yan hijirar su ka shiga, da suke da bukatuwa da taimakon kudade da kayan abinci saboda kula da ‘yan hijirar.
Kasashen sun hada Chadi, Afirka ta Tsakiya, Masar, Habasha, sai kuma kasashen Libya, Uganda da Sudan Ta Kudu.
A halin da ake ciki a yanzu ‘yan hijirar suna cin kasa da abincin da ya kamata a ce suna samu a kowace rana, kamar yadda hukumar abininci ta duniya ta sanar.
Hukumar Abincin Ta Duniya ta kuma ce; Idan har daga nan zuwa wani lokaci ba a gabatar da taimako gare ta ba, to a cikin watanni kadan ayyukan nata za su tsaya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yan hijirar
এছাড়াও পড়ুন:
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Wannan ya tayar da masa hankali, sai ya kira ‘yansanda da ke kusa da wajen.
Bayan ‘yansanda sun zo sun tono ƙasar sosai, sai suka gano wata jaririya raye tana kuka, a naɗe cikin wani yadi.
Kabiru ya ce gwamnatin ƙaramar hukumar ta ba shi damar kula da jaririyar har sai ‘yansanda sun kammala bincike.
“Na yanke shawarar kula da jaririyar ne saboda jin-ƙai da imani da ɗan Adam. Matata ma kwanan nan ta haihu, don haka za ta shayar da jaririyar,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa za su raɗa wa jaririyar suna a ranar Laraba, kuma ya riga ya sayi rago da sauran kayayyakin buƙatar suna.
Matarsa ta ce ta ji daɗi kuma za ta karɓi jaririyar hannu biyu.
A lokacin ziyarar, Hajiya Rafa’atu Hammani, tsohuwar sakatariyar dindindin ta jihar, ta ce za ta kai rahoton lamarin ga matar gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab-Nasare Idris.
Sakataren ƙungiyar GBV, Alhaji Nasiru Idris, ya ce sun kai ziyarar ne domin nuna gode wa Kabiru saboda ceton rayuwar jaririyar, da kuma gode wa Allah.
Ya kuma yaba wa ‘yansanda saboda saurin ɗaukar mataki, tare da alƙawarin cewa za su ci gaba da tallafa wa jaririyar.
Tawagar ta bai wa jaririyar kayayyaki kamar su sabulai, kayan jarirai, madarar jarirai, katifa, gado, da kuma gidan sauro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp