Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) ta sanar da cewa; Da akwai ‘yan kasar Sudan miliyan 4 da suke rayuwa a kasashen makwabta da suke fuskantar hatsarin yunwa.

Sanarwar hukumar ta kunshi cewa mutanen sun fice daga kasarsu ne tun asali saboda neman abinci da kuma mafaka daga yakin da ya barke a cikin Sudan tun a tsakiyar watan Aprilu na 2023.

 Bugu da kari sanarwar hukumar ta zo ne a matsayin gargadi saboda yadda ake samun koma bayan taimakon da ake amfani da shi wajen tafiyar da rayuwar ‘yan hijirar.

Har ila yau sanarwar ta ce; da dama daga cikin iyalan da suke isa kasashen makwabta, suna cikin gajiya da kuma rashin abinci mai gina jiki, haka nan kuma rashin isassun tufafi.

Da akwai kasashe 7 da suke makwabtaka da Sudan da ‘yan hijirar su ka shiga, da suke da bukatuwa da taimakon kudade da kayan abinci saboda kula da ‘yan hijirar.

Kasashen sun hada Chadi, Afirka ta Tsakiya, Masar, Habasha, sai kuma kasashen Libya, Uganda da Sudan Ta Kudu.

A halin da ake ciki a yanzu ‘yan hijirar suna cin kasa da abincin da ya kamata a ce suna samu a kowace rana, kamar yadda hukumar abininci ta duniya ta sanar.

Hukumar Abincin Ta Duniya ta kuma ce; Idan har daga nan zuwa wani lokaci ba a gabatar da taimako gare ta ba, to a cikin watanni kadan ayyukan nata za su tsaya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yan hijirar

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai

Akalla ’yan ci-rani 26 sun mutu bayan jiragen ruwan da suke ciki guda biyu sun nitse a teku a kusa da tsibirin Lampedusa na ƙasar Italiya.

Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce ana hasashen ƙarin wasu mutanen kuma sun ɓace yayin da ake ci gaba da aikin ceto su.

Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin Najeriya

Galibi dai ’yan ci-ranin da suka fito daga ƙasashen Afirka na ƙoƙarin tsallakawa nahiyar Turai ne domin samun ingantacciyar rayuwa.

Ko a ranar Laraba dai ma’aikatan ceto sun ce sun ceto mutum 60 da ransu, wadanda suka hada da maza 56 da kuma mata hudu, sannan aka kai su tsibirin na Lampedusa, kungiyar bayar da agaji ta Red Cross a kasar ta Italiya ta tabbatar.

Kakakin Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (IOM), Flavio Di Giacomo, ya ce akwai mutum 95 a cikin jiragen guda biyu da suka nitse.

Ya wallafa a shafukan sada zumunta cewa, “kasancewar an ceto mutum 60 da rai, ana fargabar akwai mutum 35 da suka mutu ko kuma suka ɓace.“

Hatsarin wanda ya ritsa da ’yan ci-ranin da suka taso daga ƙasar Libya shi ne na baya-bayan nan ga mutanen da ke kokarin tsallaka teku domin shiga nahiyar Turai.

Alkaluma sun nuna daga farkon shekarar nan zuwa yanzu, akalla mutum 675 ne suka rasa ransu ta irin wannan hanyar a kan iyakokin kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
  • Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
  • Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • ‘Yan Majalisa Na Ba Da Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Iya Gabatar Da Ƙudiri – Kamfani.
  • Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
  • ’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai
  • Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”
  • DAGA LARABA: Yadda sinadaran dandanon abinci ke yin illa ga lafiya