Minsitan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci ya kira yi shugaban kasar Amurka Donald Ttump da ya daina yin maganganun da ba su dace ba akan jagoran juyin musulunci Ayatullah sayyid Ali Khamnei.

Abbas Arakci ya kara da cewa; Ko kadan  Tehran ba za ta bari wani mahaluki ya ayyana mata makoma ba, idan kuwa har aka kai ta bango ta za ta bayyana hakikanin karfin da take da shi.

A jiya Juma’a ne dai shugaban kasar ta Amurka ya yi maganganu na rashin labadi akan jagoran juyin musulunci, sannan kuma ya kara da cewa, zai sake kawo wa Iran  hari idan ta koma tace sanadarin uranium.

Jamhuriyar musulunci ta Iran dai ta sha jaddada cewa ba za ta ja da baya ba akan hakkinta na tace sanadarin Uranium da cin moriyar fasahar Nukiliya ta hanyoyin zaman lafiya.

Arakci ya kuma ce; Idan har shugaban kasar ta Amurka da gaske yake akan batun tattaunawa da kai wa ga cimma wata yarjejeniya, to ya daina yin Magana da harshe na rashin ladabi akan jagoran juyin musulunci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jiniyoyin Gargadi Sun Tashi A HKI A Lokacinda Mayakan Ansarallah Suka Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kasar

An ji karar jiniyoyin gargadi a wurare da dama a HKI suna tashi bayan sun hango malamai masu linzami wadanda sojojin Yemen suka cilla daga kasar zuwa haramtacciyar kasar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kafafen yana labaran yahudawan na cewa sun yi shirin kakkabo makaman kafin su isa. Amma basu bada rahoton yawan barnan da makamai suka yi ba bayan shigowarsu haramtacciyar kasar.

Yahudawan sun bayyana cewa an ji karar jiniyar gargadi a yankunan Beersheba, Dimona da kuma garuruwan da suke kewaye da su a safiyar yau Asabar. 

Majiyar sojojin kasar Yemen sun bayyana cewa sun cilla makaman kan haramtacciyar kasar Isra’ila ne saboda ci gaba da kissan kiyashin da take a zirin gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta da Isra’ila ta kashe
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Jiniyoyin Gargadi Sun Tashi A HKI A Lokacinda Mayakan Ansarallah Suka Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kasar
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta Isra’ila ta kashe
  • Limamin Tehran:  Duniya Ce Ta Yi Yaki Da Iran
  • Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
  • Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump