Minsitan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci ya kira yi shugaban kasar Amurka Donald Ttump da ya daina yin maganganun da ba su dace ba akan jagoran juyin musulunci Ayatullah sayyid Ali Khamnei.

Abbas Arakci ya kara da cewa; Ko kadan  Tehran ba za ta bari wani mahaluki ya ayyana mata makoma ba, idan kuwa har aka kai ta bango ta za ta bayyana hakikanin karfin da take da shi.

A jiya Juma’a ne dai shugaban kasar ta Amurka ya yi maganganu na rashin labadi akan jagoran juyin musulunci, sannan kuma ya kara da cewa, zai sake kawo wa Iran  hari idan ta koma tace sanadarin uranium.

Jamhuriyar musulunci ta Iran dai ta sha jaddada cewa ba za ta ja da baya ba akan hakkinta na tace sanadarin Uranium da cin moriyar fasahar Nukiliya ta hanyoyin zaman lafiya.

Arakci ya kuma ce; Idan har shugaban kasar ta Amurka da gaske yake akan batun tattaunawa da kai wa ga cimma wata yarjejeniya, to ya daina yin Magana da harshe na rashin ladabi akan jagoran juyin musulunci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce dole ne dukkan kasashen duniya su yi kokarin kawo karshen laifukan da Isra’ila ke aikatawa a zirin Gaza da kuma kawo karshen killacewa da take yi wa yankin.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne a ranar Lahadin da ta gabata yayin da yake karbar takardar shaidar sabbin jakadun kasashen Habasha, Estonia, Djibouti, Laos, Cambodia, Burundi, Latvia, Myanmar, da Nepal.

Ya ce gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana ci gaba da  kara zafafa laifukan da take aikatawa a kan al’ummar Palastinu marasa kariya da ake zalunta a zirin Gaza.

Shugaban na Iran ya jaddada cewa: Dole ne dukkan kasashen duniya musamman kasashen musulmi su kara himma da hadin gwiwa wajen dakile wadannan laifuka a Gaza, da kuma isar da  taimako mai yawa ga mutanen Gaza.

Ya yi gargadin cewa wani “mummunan bala’i” yana faruwa a Gaza, inda Isra’ila ke kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, tare da toshe hanyoyin samun abinci, ruwa, da magunguna da sunan kare kai.

“Babban abin bakin ciki shi ne ana aikata wadannan laifuka a kan idanun wadanda ke da’awar kare hakkin bil’adama, dimokuradiyya, da ‘yancin dan adam a duniya,” in ji Pezeshkian.

Yakin Isra’ila, wanda ya fara a watan Oktoban 2023, ya yi sanadin shahadar Falasdinawa akalla 61,430 tare da jikkata sama da 153,213.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Wani Hari Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza August 11, 2025 Iran: Babu wani abu da aka yanke game da tattaunawa da Washington August 11, 2025 Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza August 11, 2025 Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari August 11, 2025 Chadi: An Daure Wani Dan Adawa Shekaru 20 A Gidan Kaso Da tara August 10, 2025 Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin August 10, 2025 Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasus Ko Rasha Bata taimaka ba August 10, 2025 HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya August 10, 2025 An Zabi Alkalan Wasa Biyu Daga Kasar Iran Don Alkalanci A gasar Kwallon Kafa ta Mata August 10, 2025 Kasar Iran Ta Yi Allah Wadai Da Bukatar ‘Yan Sahayoniyya Ta Son Kwace Zirin Gaza August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi: Mataimakin Shugaban IAEA Zai Ziyarci Tehan َA Gobe Talata
  • A Mali An Kama Sojoji Fiye da 40 Saboda Zargi da Kokarin Juyin Mulki
  • Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza
  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali
  • Iran Zata Hana Amurka Samar da Hanya A yankin Caucasusu Ko Rasha Bata taimaka ba
  • Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi
  • Tehran Times: Mai Yiwuwa Iran da Amurka su koma Tattaunawa
  • Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Katin Duba Sakamakon Jarabawa Kyauta Ga Ɗalibai