Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta
Published: 18th, May 2025 GMT
Gwamnati dai ta nisanta kanta daga labarin na karya, inda ta kwatanta batun da cewa, “mai tada hankali da rashin izini”.
Gwamnatin jihar ta kuma gargadi dukkan masu rike da mukaman siyasa da su daina bayyana ra’ayoyinsu da sunan Gwamnati kan wasu muhimman batutuwan da suka shafi siyasa ba tare da tantancewa ba.
LEADERSHIP ta fahimto cewa, wannan matakin ya biyo bayan wani labari ne da aka yada da cewa, Sanata Kwankwaso ya ki amincewa da tayin da shugaba Tinubu ya yi masa na tsunduma shi cikin jam’iyyar APC, inda ake zargin Sanatan ya bayyana cewa, ya gwammace ya bar siyasa maimakon ya koma jam’iyya mai mulki.
Ba da dadewa ba, wannan labarin na karya ya samu karbuwa a shafukan sada zumunta wanda Kwankwaso da gwamnatin Kano, tuni suka yi martani a kai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
Asusun kula da ƙananan yana na Majalisar Ɗinkin Duniya UNICEF, ya ce ya wani sabon bincike da ya gudanar ya banƙado yadda cin zarafin ƙananan yara da kuma kulle su ba bisa ƙa’ida ba ke ci gaba da bazuwa a Nijeriya.
A cikin rahoton da ya fitar ranar Litinin, UNICEF ya ce har yanzu akwai dubban ƙananan yara da gwamnati ta rufe su ba kuma tare da cikakken bayani ga iyalansu ba, wasu ma a yanzu babu cikakken bayani kan inda suke ko kuma halin da suke ciki.
Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar MajalisaAsusun ya ce a Nijeriya rufe ƙananan yara tare da yi musu shari’a ta zalunci ba bisa ƙa’ida ba na ƙara zama ruwan dare matakin da ke jefa yara cikin fargaba.
Rahoton ya ce wannan matsala ta nuna ƙarara yadda rayuwar yara ƙanana ke cikin haɗari da kuma yadda ake da ƙarancin kotuna da kuma gidajen tsare ƙananan yara.
UNICEF ɗin ya ƙara da cewa ana gwamutsa yaran a gidajen yari da manyan masu laifi sakamakon ƙananan laifuka da suka aikata abinda ke gurɓata tunaninsu a lokuta da dama kuma suke koyon wasu laifukan masu girma.
Rahoton ya ci gaba da cewa a bayanan da ya tattara a tsakanin shekarar 2018 da 2022 sama da mutane 87 ne ake tsare da su a gidajen yari haka siddan ba tare da sanin makomarsu ba, sai kuma ƙananan yara 1,279 da ake tsare da su wasu ma ba’a san inda suke ba.
Asusun ya gano cewa mafi yawan waɗannan mutane sun shafe sama da shekaru 5 a gidajen yarin, ba tare da an yanke musu hukunci ba.