Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
Published: 1st, July 2025 GMT
Tawagar likitocin kasar Sin ta 24 wadda ke jamhuriyar Nijer, ta ba da horon fasahar likitancin gargajiya ta Sin a babban asibitin Nijar dake birnin Yamai, wanda ya jawo hankulan mahalarta kusan 50, ciki har da manyan ma’aikatan kiwon lafiya na asibitin, da dalibai daga kwalejin likitanci ta jami’ar Yamai da kuma masu sha’awar likitancin gargajiya na Sin.
Zheng Zhida, shugaban tawagar likitoci ta Sin, ya bayyana a bikin kaddamar da horon cewa, tun bayan kafa cibiyar likitancin gargajiya na Sin dake babban asibitin Nijar, duban-dubatar marasa lafiya sun amfana da ita. Ya ce horon na wannan karo ba darasi ne kawai dake bada fasahohin likitanci ba, wani aiki ne na mu’ammalar al’adu.
A nasa bangare, farfesa Mamane Daou, daraktan babban asibitin Nijar, ya bayyana cewa, wannan horon ya ba da dama mai daraja ga ma’aikatan ba da jinya na asibitin wajen samun zurfin fahimtar likitancin gargajiya na Sin da kuma koyon dabaru masu amfani. Ya ce cikin ‘yan shekarun nan, likitancin gargajiya na Sin ya taimaka sosai ga yawancin marasa lafiya na Nijar bisa fa’idodin da yake da su na sauki da aminci da karancin farashi. A nan gaba, ana fatan karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu don sa kaimi ga kara amfani da fasahar likitancin gargajiya na Sin a Nijar. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: likitancin gargajiya na Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya
Kasar Venezuela ta yi kira ga Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya da ya tabbatar da cewa Amurka tana yin barazana zaman lafiyar duniya
Kasar Venezuela ta yi kira ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya amince cewa; Lallai Amurka tana yin barazana ga zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa, saboda yadda sojojin Amurka suke shisshigi a tekun Caribbean, wannan batu ya zo ne a yayin zaman gaggawa na majalisar a jiya Juma’a.
Wakilin dindindin na Venezuela a Majalisar Dinkin Duniya, Samuel Moncada, ya ce: “Suna ba da shawarar ayyuka uku ga kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya: Na farko, amincewa da barazanar zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa da sojojin Amurka suka haifar a cikin tekun Caribbean. Na biyu, daukar matakan da suka dace don hana ci gaba da tabarbarewar al’amura. Na uku, a amince da wani kuduri da ya wajabta wa dukkan mambobin su mutunta ‘yancin kai da daukan Venezuela a matsayar kasa mai cin gashin kai”.
Jami’in diflomasiyyar na Venezuela ya zargi Amurka da aiwatar da kashe-kashen gilla, yana mai cewa “gwamnatin Amurka ta amince da kai hare-haren bama-bamai kan kananan jiragen ruwa guda hudu a tekun Caribbean, inda suka kashe fararen hula 21 da ba su dauke da makamai.” Ya bayyana wadannan ayyuka a matsayin “kisa ba bisa ka’ida ba” ba na kare kai ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Amurka ta kakaba wa wasu kamfanoni 50 takunkumi saboda sayen man Iran October 10, 2025 Isra’ila ta ce yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta fara aiki October 10, 2025 Mohajirani: Iran na goyon bayan shawarar Falastinawa kan batun dakatar da bude wuta October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci