Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Published: 30th, June 2025 GMT
A bisa jagorancin Alhaji Mustapha Junaid, iyalan mamacin, da suka haɗa da matan sa da ‘ya’ya da jikokin sa, sun tarbi tawagar, kuma sun yi masu godiya.
Minista Badaru ya miƙa saƙon ta’aziyya daga Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana cewa, “Rasuwar Baba Aminu ta taɓa Shugaba Tinubu matuƙa. Yana addu’ar Allah ya yi masa sakayya da gidan Aljannar Firdausi, kuma yana ba dukkan iyalan sa haƙurin su yi jimirin jure wannan babban rashi.
Jakaden Nijeriya a Saudi Arebiya, Ambasada Ibrahim Modibbo, da Babban Jagoran Aikin Jakadanci, Ambasada Mu’azam Ibrahim Nayaya, da Jami’in Kula da Tsaro a Ofishin Jakadanci, Manjo Janar Adamu Hassan, duk suna cikin tawagar.
Malaman da aka je da su kuma duk sun yi addu’o’i ga marigayi Alhaji Aminu Ɗantata.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Yau za a yi Jana’izar Aminu Dantata a Madina
A ranar Litinin din nan za a gudanar da Sallar Jana’izar hamshakin attajiri, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu a birnin Dubai na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa.
Alhaji Aminu Dantata, wanda ke matsayin kaka ga attajirin Afirka, Alhaji Aliko Dangote, ya rasu ne bayan rashin lafiya yana da shekaru 94.
Aminiya ta ruwaito cewa Majalisar Malaman Jihar Kano, ta gudanar da sallar jana’izar marigayin ba tare da gawar ba a ranar Asabar, a Masallacin Dangi da ke Kundila Kano. Sallar ta samu halartar dubban jama’a da shugabanni daga ciki da wajen Kano.
Hakan kuwa ta faru ne bayan iyalan marigayin sun sanar bayan rasuwarsa cewa ya bar wasiyya cewa a idan Allah Ya dauki rayuwarsa, binne shi a birnin Madina ta Kasar Saudiyya.
Jana’izar Aminu Ɗantata: Abba da Sarki Sanusi sun tafi Saudiyya Tarihi da tasirin rayuwar Alhaji Aminu Alhassan DantataA ranar Lahadi, Sakatarensa, Mustapha Junaid, ya sanar cewa hukumomin Kasar Saudiyya sun bayar da izinin kai gawar Alhaji Aminu Dantata kasar domin yin jana’iza da binne shi a Madina, kamar yadda marigayin ya bar wasiyya.
Alhaji Aminu Dantata, wanda ya shahara da taimakon jama’a da ayyukan addini ne, fitaccen dan kasuwa ne a duniya, kuma tsohon dan siyasa kuma ma’aikacin gwamnati.
Tuni manyan shugabannin Nijeriya da na kasashen duniya suka fara yi wa birnin Madina na Kasaa Mai Tsarki tsinke, tare da tawagawar Gwamnatin Tarayya da da gwamnoni da Sarakunna da manyan malamai domin halartar jana’izar.
Tun bayan rasuwar Aminu Dantata shugabanni da ’yan kasuwa da daidaikun jama’a daga bangarori daban-daban suke ta tururuwar yin ta’aziyya tare da bayyana halayensa na gari da irin gudummawar da ya bayar wajen kawo ci gaba da samar da sauki ga rayuwar al’umma.