Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Published: 29th, June 2025 GMT
Alhazan da suka hada da wakilan hukumar alhazai, jami’an hukumar jin dadin alhazai ta jiha, malamai, da sauran alhazai, sun bayyana jin dadinsu ga gwamnati da hukumar alhazai bisa irin kulawar da suka samu a lokacin aikin hajjin.
Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan isowar mahajjatan, babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa, Ahmed Labbo ya bayyana jin dadinsa bisa nasarar da aka samu na dawo da alhazan jihar Jigawa Nijeriya cikin koshin lafiya.
“Mun gode wa Allah da ya dawo mana da alhazan mu lafiya,” in ji Labbo.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya ce yaki da talauci muhimmin mataki ne na hanzarta ci gaban tattalin arziki da samar da ayyukan yi.
Ya bayyana haka ne a lokacin shirin gwamnatin jihar mai taken “Gwamnati da Jama’a” wanda aka gudanar a karamar hukumar Ringim.
Malam Umar Namadi ya jaddada muhimmancin horas da matasa sana’o’in hannu da samar da yanayin kasuwanci mai kyau domin cimma wadannan manufofi.
Saboda haka, ya yi kira ga zababbun wakilai, masu rike da mukaman siyasa, shugabannin kasuwanci da sauran attajirai da su taimaka wa al’ummarsu domin kara bunkasa ci gaba da habaka tattalin arziki.
A yayin taron, Kwamishinan jin kai da harkokin musamman na jihar, Auwal Danladi Sankara, ya raba naira miliyan 50 a matsayin tallafin karfafa gwiwa ga matasa da mata sama da 250.
A cewarsa, wannan shirin tallafin kudi na musamman an kirkiro shi ne domin tallafawa kokarin Gwamna Umar Namadi wajen samar da ayyukan yi ga matasa, kirkiro sabbin ayyuka da kuma rage talauci a jihar.
Ya kara da cewa, an tsara tallafin kudin ne domin wasu su fadada kasuwancinsu, yayin da wasu kuma za su fara sabon kasuwanci na zabinsu.
Ya ce kowanne daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin ya samu naira dubu dari biyu da hamsin (₦250,000), tare da yin alkawarin ci gaba da mara wa shirin manufofi 12 na Gwamna Namadi baya, wanda aka tsara domin tabbatar da arziki da ci gaba a Jihar Jigawa.
Usman Mohammed Zaria