Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka
Published: 30th, June 2025 GMT
Rahotannin da suke fitowa daga Amurkan sun ce, wani mutum mai dauke da bindiga yankin Cotinai dake jihar Idaho ya bude wuta akan ma’aikatan kashe gobara a lokacin da suke kan aikinsu na kashe wutar da ta tashi a dajin Kootenai.
Jami’an tafiyar da sha’anin Mulki a yankin ya bayyana cewa; har yanzu ba a yi nasarar kama maharin ba,kuma yana ci gaba da kai wa jami’an tsaro hari, saboda babbar bindiga yake amfani da ita.
Bude wuta akan mai uwa da wani a kasar Amurka wata halayya ce wacce ta dade ana fama da ita saboda yaduwar makamai a hannun mutane.
Kungiyar da take kare wadanda suka makamai a cikin Amurka tana da karfin tasiri a cikin harkokin siyasar kasar fiye da sauran kungiyoyi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Hafsan Hafsoshin Sojin Iran Ya Ce: Suna Shakku Kan Tsagaita Bude Wuta Zai Dore Da Isra’ila
Manjo Janar Mousawi ya bayyana cewa: Suna shakka da kokwanto kan gaskiyar tsagaita bude wuta shin za ta dore kuwa tsakaninsu da ‘yan sahayoniyya
Babban hafsan hafsoshin sojin kasar Iran ya yi gargadin gazawar yarjejeniyar tsagaita bude wuta, yana mai nuni da rashin kwarin gwiwa kan kudurin makiya na cika alkawuran da suka dauka.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da ministan tsaron kasar Saudiyya Yarima Khalid bin Salman, babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Manjo Janar Seyyed Abdurrahim Mousawi ya bayyana cewa: Harin da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kaddamar kan kasar Iran ya zo ne duk da kamewa da kai zuciya nesa da Iran take yi, kuma a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa ba na kai tsaye ba da Amurka.
Mousavi ya bayyana cewa: Wadannan gwamnatocin biyu sun sake tabbatar da rashin amincewarsu da duk wani tsari na kasa da kasa, kamar yadda aka nunawa duniya karara a tsawon kwanaki 12 na yakin.
Ya kara da cewa: “Ba su fara yakin ba, amma sun mayar da martani ne da dukkan karfinsu, duba da irin shakkun da suke da shi kan jajircewar da makiya suka yi, ciki har da yarjejeniyar tsagaita bude wuta, amma Iran a shirye take ta kaddamar da wani muhimmin martani idan aka sake kai mata hari.”
A nasa bangaren, ministan tsaron Saudiyya Yarima Khalid bin Salman ya ce: “Ba wai kawai masarautar ta yi Allah-wadai da hare-haren ba ne, har ma ta yi kokarin kawo karshen yakin wuce gona da irin.” Haka nan kuma ya mika ta’aziyyarsa ga shahadar wasu kwamandojin sojojin Iran a yakin baya-bayan nan.