Titunan Birnin Tehran Sun Cika Makil Da Masu Jana’izar Shahidan Ta’addancin HKI
Published: 28th, June 2025 GMT
Kamfanin Dillancin Labarun “Mehr” ya nakalto cewa; Tun da jijjfin safiyar yau Asabar ne tasoshin jiragen kasa da na safa-safa su ka cika makil da masu son halarta babban filin Juyi na Tehran da can ne zai zama masonin rakiyar shahidan zuwa makwancinsu na karshe.
Ana iya ganin dubun dubatar mutane da su ka fito daga kowane bangare na al’ummar Iran domin halartar jana’izar ,yara, mata, masana da kwamandojin soja, wacce ta fara da misalin karfe 8;00 na safiyar yau agogon Tehran.
Adadin shahidan da ake jana’izar tasu a yau, sun kai 60, za kuma a rufe su ne a makabartar “Baheshti-Zahra” wacce take kunshe da shahidan juyin juya halin musulunci.
A shirnmu na rana za a ji cikakken bayani akan yadda jana’izar ta kasance.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC
Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar.
Murabus ɗin nasa ya fara aiki nan take.
Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a GombeGanduje, wanda tsohon Gwamnan Jihar Kano ne, ya bayyana rashin lafiya a matsayin dalilin da ya da ya ajiye muƙaminsa.
Ganduje ya zama Shugaban APC a watan Agustan 2023, a lokacin da jam’iyyar ke fama da rikicin cikin gida.
Lokacin da ya kwashe a matsayin shugaban jam’iyyar na cike da cece-kuce da suka.
Dalilin murabus ɗinsaKo da yake Ganduje ya ce rashin lafiya ce ta sa ya yi murabus, wasu majiyoyi sun bayyana cewa rikicin siyasa a cikin jam’iyyar ne suka tilasta masa ajiye muƙamisa.
Haka kuma, an danganta murabus ɗinsa da zarge-zargen almundahana da karkatar da kuɗaɗe.
Wasu ’ya’yan jam’iyyar sun koka cewa ofishinsa na tilasta musu biyan kuɗi da yawa, musamman masu neman tikitin takara a Abuja.
Tasirin murabus ɗinsa ga jam’iyyar APCMurabus ɗin Ganduje babban sauyi ne ga shugabancin jam’iyyar APC.
Yanzu haka, mutane da dama suna jiran su ji yadda jam’iyyar za ta shawo kan wannan lamari.
Har yanzu jam’iyyar APC ba ta fitar da wata sanarwa kan murabus ɗinsa ba.
Matsalolin da suka shafi Ganduje kan shugabancin jam’iyyarA farkon shekarar 2024, wata kotu a Jihar Kano ta hana Ganduje ci gaba da kiran kansa da ɗan jam’iyyar APC, bayan wasu shugabannin jam’iyyar sun shigar da ƙara a kansa.
Daga baya kuma, wata kotu a Abuja ta yi watsi da ƙarar da wasu ke yi don a tsige shi daga shugabancin jam’iyyar.
Zamanin Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar cike yake da rikice-rikice, kuma murabus ɗinsa yanzu zai sanya dasa ayar tambayoyi domin neman wasu amsoshi.