Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta
Published: 2nd, July 2025 GMT
Rundunar ’sanda ta jihar Delta ta ja kunnen matasan jihar a kan yin shigar banza, inda ta ce duk wanda aka kama za a iya cin shi tarar da ta kai ta naira 50,000.
A cikin wata sanarwa da Kakakin rundunar a jihar, SP Bright Edafe ya fitar ranar Talata, ya ce yin shigar banzan ya saba da dokar hana cin zarafin mutane ta (VAPP).
Kazalika sanarwar ’yan sandan ta nuna bacin rai game da shigar banza da matasa a jihar suka runguma.
“Akwai wasu daga cikin dokokin da aka kafa da mafi mutanene suka San dasu ba to Amma zamu riqa fito dasu xaya bayan xaya don a sani.
“Duk wata shiga da ke nuna tsiraicin mutum a fakaice za a ci tarar duk wanda aka kama da laifi. Gwamnatin Jihar Delta ba da wasa take ba, sannan ba ta kafa wadannan dokokin don wasa ba,” in ji sanarwar ’yan sandan.
An samar da kuma kafa dokar VAPP a shekara ta 2015 lokacin tsohon shugaban Kasa Goodluck Jonathan, kuma jihar Delta ma ta amince da dokar.
Rundunar ta ce ba iya shigar banza ba, dokar ta ku8ma hana yi wa ’ya’ya mata kaciya da cin zarafin yara marayu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Shigar banza shigar banza
এছাড়াও পড়ুন:
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Shugabannin jam’iyyar APC a matakin gunduma na Gayam, cikin ƙaramar hukumar Lafia, sun dakatar da shugaban jam’iyyar a matakin jiha, Hon. Aliyu Bello. Sun zarge shi da aikata abubuwan da suka saɓa da kundin tsarin mulki na jam’iyyar, musamman sashe na 21 (D)(i–iii), wanda ya haɗa da cin amanar jam’iyya da goyon bayan ɗan takarar wata jam’iyya daban.
Shugaban gundumar, Ibrahim Ilyasu, ya bayyana cewa matakin dakatarwar ya fara aiki nan take, kuma Hon. Bello ba zai iya wakiltar kansa ko amfani da matsayin sa a matsayinsa na mamba na APC daga Gayam ba, har sai an warware batutuwan da aka gabatar. Sun kuma zarge shi da jawo wa jam’iyyar tozarci da keta mutuncinta a idon jama’a.
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A KanoSai dai wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyar a jihar sun ce wannan matakin wani yunkuri ne daga wani ɓangare na ƙungiyar siyasa da ke ƙoƙarin kifar da Bello daga kujerarsa, musamman bisa alaƙa da wani ɗan takarar gwamna a jihar. Sun ce wannan rikici ya ƙara bayyana rabuwar kai da rikicin cikin gida a jam’iyyar.
A wata ganawa da wasu shugabannin jam’iyyar a Lafia, an kaɗa ƙuri’ar nuna goyon baya da amincewa da shugabancin Hon. Bello, wanda hakan ke nuna cewa har yanzu akwai sassa a jam’iyyar da ke goyon bayansa, duk da dakatarwar da aka sanar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp