Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta
Published: 2nd, July 2025 GMT
Rundunar ’sanda ta jihar Delta ta ja kunnen matasan jihar a kan yin shigar banza, inda ta ce duk wanda aka kama za a iya cin shi tarar da ta kai ta naira 50,000.
A cikin wata sanarwa da Kakakin rundunar a jihar, SP Bright Edafe ya fitar ranar Talata, ya ce yin shigar banzan ya saba da dokar hana cin zarafin mutane ta (VAPP).
Kazalika sanarwar ’yan sandan ta nuna bacin rai game da shigar banza da matasa a jihar suka runguma.
“Akwai wasu daga cikin dokokin da aka kafa da mafi mutanene suka San dasu ba to Amma zamu riqa fito dasu xaya bayan xaya don a sani.
“Duk wata shiga da ke nuna tsiraicin mutum a fakaice za a ci tarar duk wanda aka kama da laifi. Gwamnatin Jihar Delta ba da wasa take ba, sannan ba ta kafa wadannan dokokin don wasa ba,” in ji sanarwar ’yan sandan.
An samar da kuma kafa dokar VAPP a shekara ta 2015 lokacin tsohon shugaban Kasa Goodluck Jonathan, kuma jihar Delta ma ta amince da dokar.
Rundunar ta ce ba iya shigar banza ba, dokar ta ku8ma hana yi wa ’ya’ya mata kaciya da cin zarafin yara marayu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Shigar banza shigar banza
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Gina Asibitin Dabbobi A Jihar Kwara
Ministan Ma’aikatar Kula da Kiwon Dabbobi, Alhaji Idi Mukhtar Maiha, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta amince da gina sabon asibitin dabbobi, da cibiyar ajiye dabbobi, tare da samar da allurar rigakafi a Jihar Kwara.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin gabatar da sakamakon nazarin taswirar fadin jihar(Geospatial Mapping) da aka gudanar a Ilori babban birnin Jihar Kwara.
Da yake wakiltar Ministan, Richard Mbaram ya bayyana wannan shiri a matsayin babbar nasara a tarihi wajen samo mafita ta dindindin ga rikicin manoma da makiyaya a ƙasar nan.
Ya ce aikin na daga cikin tsare-tsaren Shirin Sauya Hanyar Kiwo na Kasa (National Livestock Transformation Plan) na tsawon shekaru goma (2019-2028) wanda ya mayar da hankali kan gyara harkar kiwo a Najeriya.
A nasa jawabin, Kwamishinan Ƙasa na L-Press, Dr. Sanusi Abubakar, ya yaba wa Jihar Kwara bisa zuba jari a bangaren ci gaban kiwo.
Ya yi alkawarin ci gaba da bai wa gwamnatin jihar goyon baya domin cimma sabon tsari a harkar kiwo.
Shi ma Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, wanda Mai ba shi Shawara na Musamman Alhaji Sa’adu Salahudeen, ya wakilta, ya yaba wa cibiyar cike ta Jami’ar Bayero Kano bisa jajircewa da ƙwarewar da suka nuna a duk tsawon aikin.
Ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta aiwatar da sakamakon binciken ba tare da kaucewa daga abin da aka gano ba.
Gwamna AbdulRazaq ya yi kira ga sarakuna, abokan hulda, hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki da su hada hannu da gwamnati wajen aiwatar da shawarwarin da binciken ya bayar.
Tun da farko a jawabinsa, Darakta a Cibiyar Harkar Noma ta Jami’ar Bayero da ke Kano, Farfesa Sanusi Muhammed, ya bayyana cewa binciken ya samar da wani dandali mai inganci don tsara ayyuka, kai agaji, da ƙirƙirar manufofi a bangaren kiwo.
Farfesa Muhammed ya yi kira ga gwamnati da ta yi amfani da bayanan taswirar wajen gyaran ruwan sha na dabbobi da ƙirƙirar tsarin samar da ruwa mai jure canjin yanayi.
ALI MUHAMMAD RABIU