Aminiya:
2025-10-13@17:49:57 GMT

Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta

Published: 2nd, July 2025 GMT

Rundunar ’sanda ta jihar Delta ta ja kunnen matasan jihar a kan yin shigar banza, inda ta ce duk wanda aka kama za a iya cin shi tarar da ta kai ta naira 50,000.

A cikin wata sanarwa da Kakakin rundunar a jihar, SP Bright Edafe ya fitar ranar Talata, ya ce yin shigar banzan ya saba da dokar hana cin zarafin mutane ta (VAPP).

Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu Za mu shige gaba idan aka dawo da tattauna shirin nukiliyar Iran — EU

Kazalika sanarwar ’yan sandan ta nuna bacin rai game da shigar banza da matasa a jihar suka runguma.

“Akwai wasu daga cikin dokokin da aka kafa da mafi mutanene suka San dasu ba to Amma zamu riqa fito dasu xaya bayan xaya don a sani.

“Duk wata shiga da ke nuna tsiraicin mutum a fakaice za a ci tarar duk wanda aka kama da laifi. Gwamnatin Jihar Delta ba da wasa take ba, sannan ba ta kafa wadannan dokokin don wasa ba,” in ji sanarwar ’yan sandan.

An samar da kuma kafa dokar VAPP a shekara ta 2015 lokacin tsohon shugaban Kasa Goodluck Jonathan, kuma jihar Delta ma ta amince da dokar.

Rundunar ta ce ba iya shigar banza ba, dokar ta ku8ma hana yi wa ’ya’ya mata kaciya da cin zarafin yara marayu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Shigar banza shigar banza

এছাড়াও পড়ুন:

Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni

A safiyar Litinin ɗin nan ƙungiyar Hamas ta saki rukunin farko na ’yan ƙasar Isra’ila bakwai da ta yi garkuwa da su a Zirin Gaza.

A ɗaya ɓangaren kuma Falsɗinawa sun yi cincirindo a yankin Gaɓar Yammacin Kogin Jordan domin tarbar ’yan uwansu kimanin 2,000 da Isra’ila za ta sako.

Tuni jami’an kungiyar agaji ta Red Cross suka shiga gidan yarin Wada a safiyar domin ɗaukar wani fursuna Bafalasdine da za fitar, wanda ke fama da rashin lafiya.

Hamas ta mika su ne ga kungiyar Red Cross a Gaza a yayin da ake da ran sako wasu ƙarin mutum 13 na gaba a Litinin ɗin nanm a cewar hukumomin Isra’ila.

Wannan na faruwa ne a yayin da Shugaban Amurka, Donald Trump, wanda ya taka muhimmiyar rawa a sulhun, yake ziyara a ƙasar Isra’ilan a safiyar Litinin.

Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku

Wannan na zuwa ne bayan yarjejeniyar zaman lafiyar da ɓangarorin biyu suka sanya hannu a kai a baya-bayan nan.

A bangare guda kuma Falsɗinawa sun yi cincirindo a yankin Gaɓar Yammacin Kogin Jordan domin tarbar ’yan uwansu kimanin 2,000 da Isra’ila za ta sako, a matsayin ɓangarenta na musayar fursunonin yaƙin.

Ma’aikatar Harkokin Gida ta Isara’ila ta fitar da jerin sunayen mutanen da aka saki da shekarunsu:

Eitan Abraham Mor, 25 Gali Berman, 28 Ziv Berman, 28 Omri Miran, 48 Alon Ohel, 24 Guy Gilboa-Dalal, 24 Matan Angrest, 22

Na gaba ake da ran muka su ga iyalansu a wani sansanin soji a Kudancin Isra’ila.

A ɗaya bangaren kuma kungiyar kula da Fursunoni ta Palastinu ta fitar da jerin sunayen mutane 1,718 da Isra’ila za ta sako.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
  • ASUU za ta fara yajin aikin mako 2 daga ranar Litinin
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta