Aminiya:
2025-10-13@18:09:52 GMT

Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu

Published: 1st, July 2025 GMT

Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi ya amince da kafa kwamitin mambobi 41 da nufin kafa sabbin masarautu a faɗin jihar.

Wata sanarwa da kakakin gwamnan, Mukhtar Gidado, ya fitar ta bayyana cewa kwamitin ya ƙunshi fitattun mambobi 41 da aka zabo daga ɓangarori daban-daban, ciki har da sarakunan gargajiya, ƙwararru, malaman jami’a, wakilan ƙungiyoyin farar hula, lauyoyi, jami’an tsaro, da ƙungiyoyin addini.

Sanarwar ta ce, “Wannan shiri ya biyo bayan kiran da gwamnatin jihar ta yi tun da farko na gayyatar al’ummomi da su gabatar da buƙatunsu na sabbin masarautun gargajiya.

“Kwamitin yana da alhakin tantance waɗannan bukatun bisa ƙa’idar adalci, daidaito, shigar da kowa cikin harkokin siyasa da zamantakewa, da ɗorewar tattalin arziki.”

Alhaji Hamza Koshe ne zai jagoranci kwamitin, tare da Mai Shari’a Habibu Idris a matsayin Mataimakin Shugaba. Sauran mambobin sun haɗa da manyan jami’an gwamnati, masu ba da shawara na musamman, da wakilai daga Ƙungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA), Ƙungiya Jama’atu Nasril Islam (JNI), Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), Kungiyar ’Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ), da kuma hukumomin tsaro daban-daban.

Farfesa Ibrahim Garba, wani masanin tarihi daga Jami’ar Maiduguri, yana cikin ƙwararrun da aka kawo don jagorantar kwamitin kan la’akari da al’adu da tarihi.

An shirya cewa Gwamna Bala Mohammed zai ƙaddamar da kwamitin ranar Alhamis, 3 ga Yuli, a Gidan Gwamnati, Bauchi, da karfe 10:00 na safe, in ji Gidado.

Ya ƙara da cewa duk wannan tsari na da nufin ƙarfafa masarautun gargajiya, inganta shigar jama’a cikin harkokin mulki, da kuma raya al’adun jihar. (NAN)

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwamiti masarautu

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

 

Ta wadanne hanyoyi cutar Kansa ke farawa?

Kowace kwayar halitta ta jikin mutum akwai aikin da take yi, asalin kwayar halittar ta kan kasu kashi-kashi; suna mutuwa idan aka fitar da su ko kuma suka lalace, sai wata kwayar ta maye gurbinsu. A irin wannan lokaci ne, Kansar ke samun gurin zama sai ta zuba tata kwayar halittar ta kori asalin kwayar halittar da ke jikin Dan’adam, wanda hakan ke jawo matsaloli a sassan jikin da Kansar ta kama.

Saboda haka, kwayar cutar Kansa; ta kan watsu a sauran sassan jiki, misali Kansar huhu ta kan tafi cikin kasusuwa ta girma, a yayin da kwayar ta yadu; ana kiranta da suna ‘meh-TAS-tuh-sis’, ita kuma Kansar huhu idan ta tafi cikin kasusuwa; ana kiran ta da suna ‘Lung Cancer’ a turance. A bangaren likitoci, kwayar cutar Kansar da ta shiga cikin kashi; daidai ta ke da ta huhu, sai dai idan ta yadu a cikin kashin.

 

Banbance-banbancen cutar Kansa:

Wata Kansar ta kan yadu ne cikin gaggawa, yayin da kuma wata ta ke yaduwa a hankali a hankali, sannan kowacce ana iya yin maganinta ta hanyoyi daban-daban, wata ta hanyar tiyata kadai za a iya samun waraka; wata kuma ta hanyar shan magani.

Idan mutum yana dauke da Kansa, likita ya kan yi kokari wajen gano irin Kansar da yake dauke da ita. Mutanen da ke da cutar Kansa, ana yi musu magani ne gwargwadon irin yanayin wadda suke dauke da ita.

 

Wane matsayi cutar Kansa ta taka?

Duk wanda ke dauke da wannan cuta ta Kansa, likita zai so sanin matakin da ta kai, daga inda ta fara ana kiran sa a turance ‘Cancer Stage’, sannan matsayin da Kansar ta ke shi ne zai taimaka wajen sanin maganin da za a dora mai dauke da lalurar a kai.

Kowace irin Kansa, akwai gwajin da ake yi domin gano matasayin da ta kai. A dokar gwajin matakinta na farko da kuma mataki na biyu, na nuna Kansar ba ta yi karfi sosai ba. Mataki na uku da na hudu kuma yana nuna ta yadu sosai. Mataki na hudu shi ne makura wajen yaduwar ta.

 

Alamomin 20 Na Kamuwa Da Cutar Kansa:

1- Shashsheka da karancin numfashi

2- Tari da ciwon kirji, alama ce ta Kansar huhu ko ta bargo ciwon kirjin kan kasance daga kirjin zuwa kafada, sannan ya sauko zuwa hannu

3- Zazzabi da saurin kamuwa da ciwo, hakan na faruwa ne dalilin asalin kwayar halittar jinin mutum ta tabu

4- Fama wajen hadiye abu, wannan na nuni da an kamu da wannan cuta

5- Futowar kurji me ruwa a wuya, hammata da kuma gwiwa

6- Yawan zubda jini

7- Kasala da yawan gajiya

8- Kumburin ciki

9- Rashin sha’awar abu da kuma daukewar dandano

10- Ciwon ciki da mara

11- Fitar jini daga dubura

12- Rama lokaci guda

13- Yawan ciwon ciki

14- Nono ya yi ja ya kumbura alama ce ta ‘breast cancer’

15- Canjawar kan nono

16- Nauyi da kuma ciwo na fitar hankali a lokacin al’ada, wannan ita ma alama ce ta ‘uterus cancer’, ana bukatar yin hoto (transbiginal)

17- Kumburin fuska

18- Canjawar farce, zai iya kasancewa ‘lung cancer’, idan kuma ya kode ya yi fari to ‘liber cancer’ ne

19- Ciwon baya a bangaren dama, yana nuni da ‘liber cancer’ ko ‘breast cancer’

20-Fesowar kuraje a jikin mutum

Amma sai an je asibiti an ga likita kafin a tabbatar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Kiwon Lafiya Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace? October 5, 2025 Kiwon Lafiya Matsalar Tasgadewar Kashin Baya September 27, 2025 Kiwon Lafiya Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja September 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar.
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya