Shugaban Karamar Hukumar Maru ta Jihar Zamfara, Alhaji Bello Mohammed Jabaka, ya yi kira ga al’ummar yankin da su dauki matakan kariya domin dakile yaduwar cutar kwalara da sauran cututtukan da ke yaduwa cikin sauri a yankin.

Ya yi wannan kiran ne yayin da yake zantawa da manema labarai a Gusau, babban birnin jihar, kan matakan da hukumar ta dauka domin dakile barkewar cutar ta amai da gudawa a wasu sassan karamar hukumar.

Alhaji Jabaka ya jaddada muhimmancin tsaftar muhalli, musamman wajen tsaftace rijiyoyi da sauran hanyoyin samun ruwan sha, wuraren da ake dafa abinci, da kuma tsaftace muhalli gaba daya, tare da tsaftar jiki wanda ya ce shi ne mabuɗin hana yaduwar cutar ta kwalara.

A cewarsa, kwalara cuta ce da za ta iya bulla a ko ina, don haka ya zama wajibi al’umma su kasance cikin shiri da lura.

Yayin da yake bayani kan halin da aka shiga, ya ce ya gaggauta bayar da umarni ga jami’an lafiya da su dauki wadanda cutar ta shafa zuwa asibitoci domin samun kulawar gaggawa kyauta.

A cewar shugaban karamar hukumar, an samu rahoton mutane sama da 27 da suka kamu da cutar, dukkaninsu kuma sun warke sun koma gida lafiya.

Ya kara da cewa duk wasu sabbin lamurra na bullar cutar an rika ba da kulawa kyauta ba tare da wata matsala ba.

“Zuwo yanzu, babu rahoton mutuwar kowa sakamakon cutar,” in ji shi.

Alhaji Jabaka ya bayyana cewa karamar hukumar ta samu wadatattun magunguna wadanda aka raba su a cibiyoyin lafiya daban-daban domin ci gaba da kula da duk wani sabon lamari na bullar cutar kyauta.

Game da matsalar tsaro a karamar hukumar Maru kuwa, shugaban karamar hukumar ya bayyana cewa ya bayar da umarnin a rika karanta Alkur’ani mai girma a kowace Juma’a da fatan Allah a kawo karshen matsalolin tsaro da suka dade suna addabar yankin.

Ya bayyana fatansa na cewa addu’o’in za su taimaka wa jami’an tsaro wajen yaki da ‘yan bindiga tare da dawo da zaman lafiya a yankunan da lamarin ya shafa.

Alhaji Jabaka ya kuma yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa ayyukan raya kasa daban-daban da ya aiwatar a karamar hukumar Maru, musamman gyaran Asibitin Gaba Daya, gina tituna da sauran ayyukan gine-gine.

Ya tabbatar wa da gwamnan da cikakken goyon baya da hadin kan al’ummar Maru domin  cigaban  Jihar Zamfara.

 

Daga Aminu Dalhatu 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwalara Maru Zamfara karamar hukumar Maru

এছাড়াও পড়ুন:

NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) a Jihar Gombe ta ce ta lalata wata babbar gonar Tabar wiwi a Karamar Hukumar Kaltungo a jihar Gombe.

Hukumar ta kuma ce ta kama miyagun kwayoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira tsakanin watan Yuni zuwa Agustan 2025.

’Yan ci-rani 26 sun nitse a teku suna ƙoƙarin tsallakawa Turai Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin Najeriya

Kwamandan Hukumar a jihar, Mallam Maijama’a Muhammad ne ya bayyana hakan a yayin wata ziyarar kulla zumunci da ya kai wa Darakta-Janar na kafar yada labarai mallakar jihar Gombe (GMC), Ibrahim Isa.

Ya ce an kama mutum 69 maza da mata da suke kokarin shigar da miyagun kwayoyi cikin jihar a wasu lokuta.

Muhammad ya kuma ce hukumar na amfani da dabarun rage samarwa da rage bukatar miyagun kwayoyi, tare da kira ga karin hadin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki.

Daga nan sai ya gode wa gwamnatin Jihar bisa bayar da motocin aiki guda biyu da gyaran ofishin hukumar, da inganta cibiyar farfado da masu shan miyagun kwayoyi

A nasa jawabin, Daktan kafar yada labaran, Ibrahim Isa, ya tabbatar wa NDLEA da goyon bayan kafar ta GMC, ciki har da bayar da lokacin watsa shirye-shirye kyauta, tare da alkawarin ci gaba da yin aiki tare wajen yakar ta’ammali da miyagun kwayoyi a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Sabunta Filin Jiragen Sama Na Ilori Zuwa Cibiyar Jigilar Kayayyaki Ta Zamani
  • Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido A Karamar Hukumar Gwiwa
  • Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno – INEC
  • Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC
  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • Kungiyar Ba Da Agaji Ta Sanar Da Yadda Cutar Kwalara Take Lashe Rayukan Mutane A Kasar Sudan
  • An Bukaci Ficewar Marasa Lafiya da Likitoci daga Wani Babban Asbiti A birnin London
  • Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
  • NDLEA ta lalata gonar tabar wiwi a Gombe