Karamar Hukumar Maru Ta Bukaci A Dauki Matakan Kariya Kan Cutar Kwalaraci
Published: 2nd, July 2025 GMT
Shugaban Karamar Hukumar Maru ta Jihar Zamfara, Alhaji Bello Mohammed Jabaka, ya yi kira ga al’ummar yankin da su dauki matakan kariya domin dakile yaduwar cutar kwalara da sauran cututtukan da ke yaduwa cikin sauri a yankin.
Ya yi wannan kiran ne yayin da yake zantawa da manema labarai a Gusau, babban birnin jihar, kan matakan da hukumar ta dauka domin dakile barkewar cutar ta amai da gudawa a wasu sassan karamar hukumar.
Alhaji Jabaka ya jaddada muhimmancin tsaftar muhalli, musamman wajen tsaftace rijiyoyi da sauran hanyoyin samun ruwan sha, wuraren da ake dafa abinci, da kuma tsaftace muhalli gaba daya, tare da tsaftar jiki wanda ya ce shi ne mabuɗin hana yaduwar cutar ta kwalara.
A cewarsa, kwalara cuta ce da za ta iya bulla a ko ina, don haka ya zama wajibi al’umma su kasance cikin shiri da lura.
Yayin da yake bayani kan halin da aka shiga, ya ce ya gaggauta bayar da umarni ga jami’an lafiya da su dauki wadanda cutar ta shafa zuwa asibitoci domin samun kulawar gaggawa kyauta.
A cewar shugaban karamar hukumar, an samu rahoton mutane sama da 27 da suka kamu da cutar, dukkaninsu kuma sun warke sun koma gida lafiya.
Ya kara da cewa duk wasu sabbin lamurra na bullar cutar an rika ba da kulawa kyauta ba tare da wata matsala ba.
“Zuwo yanzu, babu rahoton mutuwar kowa sakamakon cutar,” in ji shi.
Alhaji Jabaka ya bayyana cewa karamar hukumar ta samu wadatattun magunguna wadanda aka raba su a cibiyoyin lafiya daban-daban domin ci gaba da kula da duk wani sabon lamari na bullar cutar kyauta.
Game da matsalar tsaro a karamar hukumar Maru kuwa, shugaban karamar hukumar ya bayyana cewa ya bayar da umarnin a rika karanta Alkur’ani mai girma a kowace Juma’a da fatan Allah a kawo karshen matsalolin tsaro da suka dade suna addabar yankin.
Ya bayyana fatansa na cewa addu’o’in za su taimaka wa jami’an tsaro wajen yaki da ‘yan bindiga tare da dawo da zaman lafiya a yankunan da lamarin ya shafa.
Alhaji Jabaka ya kuma yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa ayyukan raya kasa daban-daban da ya aiwatar a karamar hukumar Maru, musamman gyaran Asibitin Gaba Daya, gina tituna da sauran ayyukan gine-gine.
Ya tabbatar wa da gwamnan da cikakken goyon baya da hadin kan al’ummar Maru domin cigaban Jihar Zamfara.
Daga Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwalara Maru Zamfara karamar hukumar Maru
এছাড়াও পড়ুন:
JMI Ta Bukaci Kungiyar Majalisun Dokoki Ta Duniya Su Kori HKI Daga Cikinta
Shugaban tawagar Iran a kungiyar hada kan majalisun dokokin kasashen duniya ya bukaci kungiyar ta yi tir da HKI saboda hare-haren da ta kai mata wanda ya keta dokokin kasa da kasa, ya kuma bukaci a koreta daga kungiyar.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Manoorchehr Mottaki yana fadar haka a wata wasikar da ya aikewa shugaban kungiyar majalisun dokokin ta duniya wato IPU, shugaban Tulia Ackson, ya ce abin fata shi ne kungiyar zata yi tir da HKI kan sabawa doka ta 2(4) na MDD.
Har’ila yau Mottaki ya bayyana cewa yana fatan Ackson zai sa a jingine samuwar HKI a kungiyar.
Ya ce majalisar majalisun ta tattauna dangane da hare-haren Amurka da HKI kan kasar Iran su kumka yi All..wadai da su.