Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Published: 2nd, July 2025 GMT
“Ba za su samu tayin da ya fi wannan ba abu zai ƙara muni idan suka ƙi.”
Har yanzu babu martani daga jami’an Isra’ila kan iƙirarin Trump ba.
Tattaunawar neman tsagaita wuta ta tsaya cak tun watanni da suka gabata saboda rashin jituwa kan matakin da za a ɗauka bayan an daina faɗa.
Isra’ila tana son ta ci gaba da samun damar kai farmaki idan ta ga dama, amma Hamas tana so a daina faɗa gaba ɗaya.
Ana sa ran Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, zai kai ziyara fadar White House a mako mai zuwa.
Trump ya ce zai yi magana da Netanyahu domin ganin an kawo ƙarshen yaƙin.
A farkon shekarar nan, wani ƙoƙari na tsagaita wuta ya rushe a watan Maris bayan Isra’ila ta kai wani farmaki ba tare da sanarwa ba a Gaza wanda rahotanni suka ce ya hallaka fiye da mutane 300.
Daga baya Netanyahu ya kare farmakin, inda ya bayyana cewa Hamas ta ƙi sakin fursunon Isra’ila da ke hannunta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila na neman ƙulla hulɗa da Siriya da Lebanon
Isra’ila ta bayyana shirin ƙulla hulɗa ta diflomasiyya da ƙasashen Siriya da Lebanon da suka daɗe ba sa ga maciji da juna a yankin Gabas ta Tsakiya.
Wannan na zuwa ne bayan samun lafawar rikici tsakanin Isra’ila da Iran.
Kasar Isra’ila ta ce za ta ƙulla hulɗa da ƙasashen da suka daɗe suna zaman doya da man ja, amma ta ce babu batun tattauna makomar tuddan Golan da ta ƙwace daga hannun Siriya.
Zan yi takara a Zaɓen 2027 — Peter Obi An sanya dokar hana fita a KadunaMinistan Harkokin Wajen Isra’ila, Gideon Saar wanda ya bayyana hakan a wannan Litinin din ya ce ƙasarsa tana da yaƙini kan karya lagon ƙasar Iran lokacin fito na fito na tsawon kwanaki 12 da suka yi a bayan nan.
Dangane da hakan ne Isra’ilan ke cewa za ta ƙara ƙulla hulɗa ta diflomasiyya da ƙasashen yankin.
A shekara ta 2020 Isra’ila da ƙulla hulda da kasashe da dama na Laraba na Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain gami da Maroko da ke zama karo na farko, bayan wadda Isra’ila ta ƙulla da Jordan a shekarar 1994, da kuma wadda aka fara yi da Masar a shekarar 1979.