Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Published: 2nd, July 2025 GMT
“Ba za su samu tayin da ya fi wannan ba abu zai ƙara muni idan suka ƙi.”
Har yanzu babu martani daga jami’an Isra’ila kan iƙirarin Trump ba.
Tattaunawar neman tsagaita wuta ta tsaya cak tun watanni da suka gabata saboda rashin jituwa kan matakin da za a ɗauka bayan an daina faɗa.
Isra’ila tana son ta ci gaba da samun damar kai farmaki idan ta ga dama, amma Hamas tana so a daina faɗa gaba ɗaya.
Ana sa ran Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, zai kai ziyara fadar White House a mako mai zuwa.
Trump ya ce zai yi magana da Netanyahu domin ganin an kawo ƙarshen yaƙin.
A farkon shekarar nan, wani ƙoƙari na tsagaita wuta ya rushe a watan Maris bayan Isra’ila ta kai wani farmaki ba tare da sanarwa ba a Gaza wanda rahotanni suka ce ya hallaka fiye da mutane 300.
Daga baya Netanyahu ya kare farmakin, inda ya bayyana cewa Hamas ta ƙi sakin fursunon Isra’ila da ke hannunta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya October 10, 2025
Daga Birnin Sin CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa October 10, 2025
Daga Birnin Sin Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka October 10, 2025