Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya bayyana wasu abubuwan da suka faru biyo bayan rashin lafiyar marigayi Shugaba Umaru Musa ’Yar’Adua, waɗanda suka haddasa ruɗani a faɗin Najeriya.

Jonathan, ya ce ya shirya ya mutu a fadar shugaban ƙasa maimakon ya bar muƙaminsa a lokacin da aka shiga ruɗani saboda rashin dawowar ’Yar’Adua.

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Aminu Ɗantata a Kano Za a binne Aminu Ɗantata a Madina — Iyalansa

A wata hira da aka yi da shi a Rainbow Book Club, Jonathan ya bayyana cewa Yar’Adua ya rubuta wasiƙa don miƙa masa mulki, amma wani na hannun damar shugaban ƙasa ya ɓoye wasiƙar, bai miƙa ta ga majalisa ba.

“Wannan wasiƙar an rubuta ta. Amma wanda aka bai wa, ba zan faɗi sunansa ba, ya ƙi ya miƙa ta ga majalisar ƙasa,” in ji Jonathan.

A ƙarshen shekarar 2009, ’Yar’Adua ya tafi ƙasashen waje neman magani ba tare da sanar da majalisa ba ko kuma miƙa mulki ga Jonathan kamar yadda doka ta tanada.

Wannan lamari ya jefa ƙasar cikin rikicin siyasa da na kundin tsarin mulki.

Jonathan, wanda shi ne mataimakin shugaban ƙasa a lokacin, ya ce ƙasar ta shiga wani mawuyacin hali da rabuwar kai.

“Ƙasar ta shiga tashin hankali. Rikicin Arewa da Kudu, Kirista da Musulmi ya yi tsanani. Kowace rana ina jin jita-jitar juyin mulki,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa akwai fahimtar juna amma ba a rubuta cewa Arewa za ta ci gaba da mulki na tsawon shekaru takwas bayan Obasanjo daga Kudu ya kammala mulkinsa.

Amma rashin lafiyar ’Yar’Adua ya kawo cikas.

“Rashin lafiyar ce matsala. Wannan ne ya sa har ba su so a bar ni na riƙe muƙamin shugaban ƙasa na wucin gadi,” in ji shi.

Ya ce duk da yake yana gudanar da wasu ayyuka na mataimaki, rashin wasiƙar miƙa mulki ya hana shi zama cikakken shugaban ƙasa.

“Shugaban ƙasa na da manyan nauyi guda biyu. Na farko, kai ne babban jami’in gwamnati, kamar Firaminista, wanda mataimakin shugaban ƙasa zai iya maye gurbinsa.

“Amma ba a samu kwamandan rundunar soji ba, kuma babu wani abu da ake kira kwamanda na wucin gadi,” in ji shi.

Wannan rashin tabbas ne ya sa Majalisar Ƙasa ta yi amfani da “Ƙa’idar Dole” (Doctrine of Necessity) don ba shi ikon zama shugaban ƙasa na wucin gadi a watan Fabrairun 2010.

Jonathan ya tuna irin matsin lambar da ya sha.

Ya ce wasu daga cikin abokansa sun shawarce shi da ya bar fadar shugaban ƙasa saboda tsoron ka da a kashe shi.

“Na tuna wata rana, ina mataimakin shugaban ƙasa, wani abokina ya ce ce, ‘Ka bar gidan gwamnati, ka zo ka kwana a gidan baƙina.’

“Na ce, ‘A’a. Zan kwana a fadar gwamnati. Idan akwai wanda zai kashe ni, to su kashe ni a gidan gwamnati domin ’yan Najeriya su sani an kashe ni a fadar shugaban ƙasa.’”

“Sun san ban aikata laifi ba. Idan na je na kwana a gidanka, a can aka kashe ni, za su fara cewa wasu ’yan Indiya ne suka kawo tuffa suka kashe ni. Ban so a ƙirƙiri irin wannan labari,” in ji shi.

Wannan lokaci na daga cikin mafi muhimmanci a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya.

Daga bisani, Jonathan ya zama cikakken shugaban ƙasa bayan rasuwar ’Yar’Adua a watan Mayun shekarar 2010.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rashin lafiya Siyasa Yar adua Yar Adua ya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta samu nasarar ceto mutum 10 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su tsawon watanni huɗu da suka gabata a Ƙaramar Hukumar Kagarko.

A cikin sanarwar da kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya bayyana cewa daga cikin waɗanda aka ceto har da yara masu shekaru ɗaya, uku da kuma 13.

Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro

DSP Mansir, ya ce ’yan bindigar sun kai farmaki ƙauyen Kushe Makaranta, inda suka sace mutanen daga gidajensu sannan suka kai su dajin da ke kusa da Rijana.

Rundunar, ta ce aikin ceto mutanen ya samu ne ta haɗin gwiwar ’yan sanda, jami’an DSS, da kuma sojoji.

Wani mazaunin yankin ya shaida cewa suna matuƙar farin ciki da wannan nasara, musamman ganin cewa mutanen sun kwashe watanni a hannun ’yan bindiga cikin tsananin wahala.

Hukumomin tsaro sun ce ana ci gaba da bincike domin kamo sauran ‘yan bindigar da suka tsere, tare da inganta matakan tsaro a yankin don kauce wa sake faruwar irin wannan lamarin.

“Za mu ci gaba da aiki tare da sauran hukumomi don tabbatar da cewa babu wata ƙungiyar ‘yan ta’adda da za ta samu mafaka a Kaduna,” in ji DSP Mansir Hassan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole