“Muna bayar da wannan a matsayin gargadi kai tsaye ga gwamnatin Nijeriya a matakin tarayya da na jihohi. Ka da a bari a zubar da jinin wadannan ‘yan Nijeriya marasa laifi ya tafi a banza.”

Shittu, ya lura da cewa hakurin al’ummomin da ake ci gaba da yi wa kisan gilla ba shi da iyaka, ya kara da cewa rashin kamawa da gurfanar da masu aikata laifukan tare da hukuntansu yana nuna gazawar gwamnati.

“Muna bukatar a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa, kuma na gaskiya kan wannan kisan kiyashi da kamawa tare da gurfanar da duk wadanda ke da alhakin wannan danyen aikin.

 “Muna san a biya isasshiyar diyya ga iyalan wadanda abin ya shafa, haka kuma a tura jami’an tsaro na dindindin a duk wuraren da ake kisa a Filato da jihohin makwabta.

“Akwai bukatar gwamnatin tarayya ta kara zage damtse na ganin ta magance yawaitar kashe-kashen da ake yi a fadin kasar nan baki daya” in ji sanarwar. 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Zazzau ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin aure da aka kashe a Jihar Filato.

Tun da farko, Hakimin Basawa, Haruna Abubakar ne, ya wakilci Sarkin lokacin da lamarin ya faru, saboda Sarkin ya yi tafiya.

Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC

Sarkin, ya bayyana baƙin cikinsa bisa wannan mummunan lamari, inda ya roƙi iyalan da su ɗauki wannan a matsayin ƙaddara.

Ya yaba da yadda suka yi haƙuri kuma suka bar komai ga hukuma, ba tare da ɗaukae doka a hannunsu ba.

Sarkin ya kuma tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kaduna na ƙoƙarin ganin an bi wa waɗanda abin ya shafa haƙƙinsu.

Ya ƙara da cewa zaman lafiya da haƙuri su ne mafita ga duk wata matsala, kuma hakan zai kawo ci gaba a tsakanin al’umma.

A yayin ziyarar, Sarkin ya samu rakiyar wasu daga cikin ’yan majalisarsa da hakimai.

Ya sake roƙon jama’a da su ci gaba da zaman lafiya tare da miƙa lamarin ga Allah.

Da yake magana a madadin iyalan garin, Mallam Muhammadu Dan Bami, ya gode wa Sarkin bisa ziyarar da ya kawo, tare da bayyana cewa mutanen garin masu bin doka da son zaman lafiya ne.

Daga ƙarshe, ya roƙi Sarkin da ya taimaka wajen ganin gwamnati ta cika alƙawarin da ta ɗauka na bi masu haƙƙinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’
  • Sarkin Zazzau ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
  • Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
  • Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)
  • Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum
  • Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno