Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda, Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Published: 1st, July 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
Wani sabon rikici ya barke a jihar Sokoto inda ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci a kauyen Marnouna da ke karamar hukumar Wurno, inda suka kashe akalla mutum daya tare da yin awon gaba da wasu da ba a tantance adadinsu ba a lokacin da ake sallar isha.
Shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Sokoto, Alhaji Isah Sadik Achida, wanda ya fito daga yankin ya tabbatar da faruwar harin inda ya jaddada cewa maharan sun kuma kashe shugaban kungiyar masu sayar da babura na yankin a yayin farmakin.
Achida ya ci gaba da cewa, kwana biyu kacal kafin harin masallacin, ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyuka biyu da ke makwabtaka da su, Gidan Taru da Kwargaba, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna garin tare da jaddada cewa ‘yan bindigar sun kuma kashe wani dan uwa tare da kama iyalansa baki daya.
A cewar shugaban jam’iyyar APC, ‘yan ta’addan na kokarin kafa sansani a yankin domin fadada ayyukansu.
Achida ya tabbatar wa mazauna jihar cewa gwamnatin jihar da jami’an tsaro suna bakin kokarinsu domin yakar matsalar.
Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sakkwato, ASP Abubakar Rufa’i, ya tabbatar wa gidan rediyon Najeriya faruwar lamarin inda ya ce a yanzu ‘yan fashin na kai hare-hare a lokutan damina domin kai hare-haren ba tare da an gano su ba.
NASIR MALALI