Aminiya:
2025-10-13@18:05:31 GMT

Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta Isra’ila ta kashe

Published: 28th, June 2025 GMT

Iran ta gudanar da gagarumin jana’izar tare da karramawq ga kwamandojinta da masana kimiyyar nukiliya da wasu ’yan kasar da Isra’ila ta kashe a yankin kwana 12 da aka gwabza a tsakanin ƙasashen.

Iran ta shirya gagarumin jana’izar a ƙwaryar birnin Tehran kwana huɗu bayan Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin da ɓangarorin biyu ke iƙirarin nasara a yaƙin da aka fara ranar 13 ga Yuni, 2025.

A safiyar Asabar daruruwan dubban mutane ne suka fito ɗauke da tutocin ƙasar suna wake-waken jinjina domin karrama kwamandojin da suka kwanta dama a wurin jana’izar.

Mutanen sun kuma riƙa daga hotunan mamatan a matsayin waɗanda suka yi mutuwar shahada, a yayin da suke la’antar Isra’ila da Amurka.

Daga cikin kwamandojin da Isra’ila ta kashen har da jagoran Rundunar Juyin Juya Halin Musulunci na Iran Janar Hossein Salami da Janar Amir Ali Hajizadeh da wani ƙwararren masanin kimiyyar makamashin nukiliya, Mohammad Mehdi Tehranchi.

Za a iya tuna cewa Amurka ta kai wa cibiyoyin nukiliyar Iran hare-hare a ƙarshen makon da ya gabata, kafin daga bisani a tsagaita wuta.

Amurka da Isra’ila sun yi iƙirarin cewa hare-haren sun yi gagarumar nasarar ruguza shirin kera makaman nukiliya na Iran.

Amma daga bisani Iran ta ƙaryata su, da cewa babu wata illa da hare-haren suka yi wa shirinta da makamashin nukiliya.

A ranar Talata Shugaban addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya karyata abin da ya kira kambama harin da shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya yi na cewa harin hare-haren sun mayar da shirin nukiliyar Iran baya da shekaru.

An kashe manyan sojojin da masa kimiyyar nukiliyar Iran ne a harin da Isra’ila ta fara kaiwa bisa hujjar neman daƙile shirin Iran na mallakar makamin nukiliya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila nukiliya da Isra ila Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno

Rundunar sojin Najeriya, ta bayyana cewa dakarunta sun kashe ’yan ta’adda biyar a wani samame da suka kai yankin Magumeri da Gajiram, a Jihar Borno.

Kakakin rundunar Operation Haɗin Kai, Kanar Sani Uba, ya ce dakarun sun yi arangama da wasu ’yan ta’adda 24 da ke tafe a ƙafa a ranar Juma’a.

Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina

A cewar sanarwar da ya fitar, sojojin sun yi nasarar kashe biyar daga cikinsu tare da ƙwato kuɗi Naira miliyan biyar.

“An hangi ’yan ta’addan suna ƙone gidaje da kuma kai wa mutane hari, sai dakarun suka fara bin su, inda suka tsere zuwa ƙauyen Damjiyakiri,” in ji Kanar Sani.

Ya ƙara da cewa bayan awanni huɗu ana bin su, sojoji suka sake kai musu farmaki, inda suka kashe biyar daga cikinsu, sauran 19 kuma suka tsere da raunuka.

Abubuwan da aka ƙwato daga hannunsu, sun haɗa da bindiga ƙirar AK-47, jakar harsashi gyda biyar, waya guda ɗaya da wuƙa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba
  • Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • Iran Ta Bukaci HKI Ta Aiwatar Da Yarjeniya Da Gaza Kamar Yadda Take
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza