Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
Published: 2nd, July 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Sun kuduri aniyar kare kan iyakokin Iran da tsaron kasar da kuma al’ummarta
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya ce: “Suna goyon bayan zaman lafiya, kuma ba su amince da yaki ba, amma a lokaci guda kuma, suna tabbatar da aniyarsu ta kare kan iyakokin Iran da tsaron kasarta da kuma al’ummarta.
A yau, Laraba ne, Shugaban kasar Iran Pezeshkian ya wallafa wani rubutu a shafinsa na sadarwa, inda ya jaddada babban kudirin gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na kare kan iyakokin kasar da tsaro da al’ummar kasar. Yana mai jaddada cewa: “A tushen al’adu da wayewar Iran, suna da gogewa da yawa wajen rage wahalhalun da mutane ke fuskanta.”
Shugaban ya kara da cewa: Iran na cike da kayan ado da kyau kuma gaskiya tana bayyana a kowane lungu da sako, a ko da yaushe suna neman gina gadoji ne tare da wasu, ba katanga ba.
A gefen taron Majalisar ministocin kasar, shugaba Pezeshkian ya ce: “A kwanakin nan tunaninsu ya fi karkata ne wajen magance matsalolin al’ummar kasa da kuma rage damuwarsu tare da jaddada wajibcin yin aiki tare a tsakanin al’ummar Iran don kaucewa jefa su cikin matsaloli; Ya kara da cewa: Al’ummar Iran sun nuna jajircewa da hadin kai wajen samar da alfahari da daukaka ga kansu, kuma sun yi nasarar dakile makircin makiya, kuma hakan ya cancanci a yaba musu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Shugaban kasar Iran
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa
JMI ta bawa kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen makamai masu linzami wadanda ake iya cillasu daga cikin tekuna mai suna Ghadr.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya ce makamai mai linzami samfurin Ghadir wanda ake iya cilla shi daga cikin teku ya shiga hannun sojojin kasar Yemen sannan bisa bayanan wasu kasashen yamma hakan wani hatsari ne ga kasashen Amurka da kawayenta a yankin, musamman HKI.
Makamin wanda ake iya cillashi daga tekun red sea yana yin barna mai yawa ga makaman makiya. Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran bata yi wani karin bayani dangane da wannan labarin ba, majiyar ofishin daraktan tsaron kasa na Amurka ta bayyana cewa, JMI tana ta fi ko wace kasa a yankin mallakan makamai masu linzami kuma sune a gaba a duniya wajen kera jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga Nesa.