Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta da Isra’ila ta kashe
Published: 28th, June 2025 GMT
Iran ta gudanar da gagarumin jana’izar tare da karramawq ga kwamandojinta da masana kimiyyar nukiliya da wasu ’yan kasar da Isra’ila ta kashe a yankin kwana 12 da aka gwabza a tsakanin ƙasashen.
Iran ta shirya gagarumin jana’izar a ƙwaryar birnin Tehran kwana huɗu bayan Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin da ɓangarorin biyu ke iƙirarin nasara a yaƙin da aka fara ranar 13 ga Yuni, 2025.
A safiyar Asabar daruruwan dubban mutane ne suka fito ɗauke da tutocin ƙasar suna wake-waken jinjina domin karrama kwamandojin da suka kwanta dama a wurin jana’izar.
Mutanen sun kuma riƙa daga hotunan mamatan a matsayin waɗanda suka yi mutuwar shahada, a yayin da suke la’antar Isra’ila da Amurka.
Daga cikin kwamandojin da Isra’ila ta kashen har da jagoran Rundunar Juyin Juya Halin Musulunci na Iran Janar Hossein Salami da Janar Amir Ali Hajizadeh da wani ƙwararren masanin kimiyyar makamashin nukiliya, Mohammad Mehdi Tehranchi.
Za a iya tuna cewa Amurka ta kai wa cibiyoyin nukiliyar Iran hare-hare a ƙarshen makon da ya gabata, kafin daga bisani a tsagaita wuta.
Amurka da Isra’ila sun yi iƙirarin cewa hare-haren sun yi gagarumar nasarar ruguza shirin kera makaman nukiliya na Iran.
Amma daga bisani Iran ta ƙaryata su, da cewa babu wata illa da hare-haren suka yi wa shirinta da makamashin nukiliya.
A ranar Talata Shugaban addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya karyata abin da ya kira kambama harin da shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya yi na cewa harin hare-haren sun mayar da shirin nukiliyar Iran baya da shekaru.
An kashe manyan sojojin da masa kimiyyar nukiliyar Iran ne a harin da Isra’ila ta fara kaiwa bisa hujjar neman daƙile shirin Iran na mallakar makamin nukiliya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Iran Isra ila nukiliya da Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Ta Kashe ‘Yan jaridar Al Jazeera Biyar A Gaza
Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta kashe wani fitaccen dan jarida na kafar yada labarai ta Al Jazeera Anas al-Sharif tare da abokan aikinsa hudu a wani hari da ta kai Gaza.
Isra’ila ta zarge shi da kasancewa wani jagora na Hamas sannan ta ce ta hallaka shi saboda irin rahotannin da yake bayarwa masu tsanani daga arewacin Gaza.
Isra’ila ta hari ‘yan jaridar biyar – Anas al-Sharif wanda shi ne fitacce tare da Mohammed Qreiqeh masu aikawa da rahotanni ne sai kuma masu daukar musu hoto Ibrahim Zaher da Mohammed Noufal da kuma Moamen Aliwa wadanda dukkanin su suna aiki ne da kafar ta Al Jazeera.
A lokacin da Isra’ila ta kai musu harin ta sama suna cikin wani tanti ne na ‘yan jarida da ke wajen asibitin al-Shifa a birnin na Gaza.
Isra’ilar ta ce kisan hukunci ne na irin rahotannin da Anas din ya ke aika wa Al Jazeera da ke arewacin Gaza.
Baya haka Isra’ila ta kuma ce dan jaridar wani jigo ne na wani reshe na kungiyar Hamas da ke shirya hare-haren makaman roka da Hamas ke kai mata – zargin da Al Jazeera ta musanta.
A sanarwar da ta fitar rundunar sojin Isra’ilar ta zargi al-Sharif da fakewa a matsayin dan jarida- tana zarginsa da hannu wajen kai mata hare-hare da makaman roka kann fararen hula da sojojinta.
Ta ce a baya ta fitar da wasu bayanan sirri da ke tabbatar da alakarsa da ayyunakn soji na Hamas, ciki har da jerin horon ta’addanci da ya halarta.
Sanarwar ta kara da cewa kafin harin sojin na Isra’ila sun dauki matakai na kauce wa illata farar hulha.
Mako biyu da ya wuce Al Jazeera ta soki rundunar sojojin ta Isra’ila kan abin da ta kira kokarin tunzura masu aika mata da rahotanni a Gaza ciki har da al-Sharif.
Kungiyoyin kare hakkin dan’adam sun ce Isra’ila ta kashe ‚yan jarida sama da dari biyu (200) a Gaza tun daga watan Oktoba na 2023, kan abin da suka ce yunkuri ne na hana bayar da rahotannin zargin cin zarafin da Isra’ila ke yi a Gaza.
Isra’ila dai ta hana ‘yan jarida na waje aikawa da rahotanni a fili daga yankin.
Jim kadan bayan harin ne Isra’ila ta fitar da wata sanarwa da a ciki take tabbatar da kai harin da ta ce ta hallaka Anas al.-Sharif, tana mai cewa wani jagora ne a Hamas.
Rundunar sojin ta Isra’ila ba ta ambaci sauran ‘yan jaridar da ta kashe su tare ba.
Al-Sharif, mai shekara 28, yana rubuta sakonni ne ta shafin X, jim kadan kafin mutuwarsa – inda a ciki yake gargadi kan ruwan bama-bamai da Isra’ila ke yi a birnin na Gaza.
BBC ta ga wasu hotunan bidiyo masu tayar da hankali wadanda kuma ta tabbatar da sahihancinsu, na bayan harin da ya hallaka ‘yan jaridar, inda a ciki ake iya ganin mutane na dauke gawawwakin.
BBC/Hausa