Aminiya:
2025-08-14@19:44:55 GMT

An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina

Published: 29th, June 2025 GMT

Gwamnatin Saudiyya ta amince a yi jana’iza tare da binne gawar attajirin ɗan kasuwar nan na Kano, Alhaji Aminu Alhassan Dantata.

Babban sakataren marigayin, Mustapha Abdullahi Junaid ya ce shirye-shirye sun kammala domin gudanar da jana’iza tare da binne gawar marigayin a garin Madina.

A wani saƙo da Mustapha ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bayyana cewa, “AlhamdulilLah an samu amincewar (hukumomi).

“Za a ɗauki Aminu Alhassan Ɗantata daga Abu Dhabi zuwa Madina. Za a yi jana’iza gobe da safe in sha Allah.”

Aminiya ta ruwaito cewa a safiyar jiya Asabar ce dai attajirin ɗan kasuwar ya rasu a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.

Amma iyalansa suka jinkirta binne shi domin a cewarsu, suna so ne su cika masa burinsa na binne gawarsa a garin na Madina, birnin Ma’aiki (S.A.W).

An dai gudanar masa da sallar gawa da ba ta kusa wata sallar ga’ib a Jihar Kano, wadda Sheikh Ibrahim Khalil ya jagoranta.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun

Rundunar ’yan sanda a Jihar Ogun ta ce, ta kama wani mai babur mai suna Kadir Owolabi, yana ɗauke da ƙoƙon kan mutane uku.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Omolola Odutola ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a Abeokuta ranar Talata.

Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9 Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ

Odutola ta ce, binciken da jami’an ’yan sandan tafi da gidanka suka yi a jakar wanda ake zargin, ya kai ga gano wasu kan mutane guda uku.

Ta ce, jami’an tsaro ne suka gudanar da aikin bincike na yau da kullum daga rundunar ’yan sanda na tafi da gidanka na 71 PMF, a yankin Awa da ke Ijebu, da ƙarfe 2:00 na rana.

A ranar Litinin, a kan babbar titin Ijebu Ode zuwa Ibadan a mahaɗar ’yan gudun hijira, Oru Ijebu.

“A yayin atisayen, jami’an sun cafke Kadir Owolabi wanda ke kan babur, inda aka gudanar da bincike a kan jakunkunansa, an gano wasu kan mutane guda uku.

“Bincike na farko ya kai ga kama wani wanda ake zargi, mai suna Jamiu Yisa, mai shekara 53, a bayan sakatariyar Ƙaramar hukumar Ijebu Ode,” in ji ta.

Odutola ta ce, Kwamishinan ’yan sanda jihar, Lanre Ogunlowo ya umurci hukumar binciken manyan laifuka ta jihar da ta ɗauki ragamar lamarin domin gudanar da bincike mai zurfi.

Kakakin rundunar ta ƙara da cewa, rundunar ta sake jaddada aniyarta na ɗaukar ƙwararan matakai na yaƙi da miyagun laifuka, ta kuma  buƙaci mazauna yankin da su ba ’yan sanda haɗin kai tare da ba jama’a tabbacin amincewa da su da kuma basu kariyar sirri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
  • An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 127
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 125
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 124
  • ETFund Ta Koka Kan Gibin Da Ake Samu A Sashin Lafiyar Najeriya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato Tambuwal kan zargin N189bn
  • An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK