An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina
Published: 29th, June 2025 GMT
Gwamnatin Saudiyya ta amince a yi jana’iza tare da binne gawar attajirin ɗan kasuwar nan na Kano, Alhaji Aminu Alhassan Dantata.
Babban sakataren marigayin, Mustapha Abdullahi Junaid ya ce shirye-shirye sun kammala domin gudanar da jana’iza tare da binne gawar marigayin a garin Madina.
A wani saƙo da Mustapha ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bayyana cewa, “AlhamdulilLah an samu amincewar (hukumomi).
“Za a ɗauki Aminu Alhassan Ɗantata daga Abu Dhabi zuwa Madina. Za a yi jana’iza gobe da safe in sha Allah.”
Aminiya ta ruwaito cewa a safiyar jiya Asabar ce dai attajirin ɗan kasuwar ya rasu a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.
Amma iyalansa suka jinkirta binne shi domin a cewarsu, suna so ne su cika masa burinsa na binne gawarsa a garin na Madina, birnin Ma’aiki (S.A.W).
An dai gudanar masa da sallar gawa da ba ta kusa wata sallar ga’ib a Jihar Kano, wadda Sheikh Ibrahim Khalil ya jagoranta.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Za a birne Aminu Ɗantata a Madina – Iyalansa
Iyalan marigayi Alhaji Aminu Ɗantata, wanda ya rasu, sun bayyana cewa ya bar wasiyyar cewa a birne shi a Birnin Madina na ƙasar Saudiyya.
Majiyoyi daga cikin iyalansa sun bayyana cewa marigayin ya buƙaci a birne shi kusa da uwargidansa a Madina a duk lokacin da ya rasu.
Mangu: Gwamnatin Filato ba ta aiko da wakilai don yin ta’aziyya ba — Sarkin Zazzau ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’A gefe guda kuma, Majalisar Malamai ta Jihar Kano ta yi wa marigayin sallar Ga’ib a Masallacin Aliyu bin Abu Talib da ke unguwar Dangi.
Cikin wata sanarwa da ta fitar, majalisar ta bayyana cewa za a yi masa sallar ne duk d gawarsa na Birnin Dubai, na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa.
An gudanar da sallar a cikin birnin Kano, da misalin ƙarfe 2 na rana.
Sanarwar ta buƙaci al’umma da su halarta domin yin sallar da kuma yi wa marigayin addu’o’i.
Alhaji Aminu Ɗantata ya rasu yana da shekaru 94 bayan fama da rashin lafiya.
Ya rasu yana da ’ya’ya bakwai da jikoki da dama.
Babban sakatarensa, Mustapha Abdullahi Junaid, ne ya sanar da rasuwar a safiyar Asabar.
Ɗaya daga cikin attajirai mafiya arziƙi a Nahiyar Afirka, ya rasu ne a ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE.)
Alhaji Aminu Ɗantata shi ne mai kamfanin mai na Express Petroleum & Gas, kuma a matsayin uba yake ga attajirin Afirka, Alhaji Aliko Ɗangote.