Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Published: 2nd, July 2025 GMT
Ya ce kamar yadda mutane suka karanta a jarida, shi ma ya karanta, amma babu gaskiya cikin batun.
Ya ce a yanzu, kowa ya san yana cikin PDP kuma yana da matsayi a jam’iyyar, bai bar ta ba kuma da yardar Allah zai ci gaba da zama a cikinta.
Ya ce dalilin da ya sa wasu ke son ya koma APC shi ne domin jam’iyyar APC a Filato ba ta da shugabanni nagari, shi ya sa suke kallon shugabannin PDP da fatan su shiga jam’iyyar domin kawo gyara.
Ya ƙara da cewa wasu daga cikin mambobin APC na ƙasa suna sha’awar abubuwan da PDP ta yi a Filato, kuma suna ganin irin waɗannan ayyuka na buƙatar shugabanni masu nagarta.
Amma ya ce su dai suna sa Allah a gaba a siyasa da kuma a cikin jama’a, kuma duk inda Allah Ya nufa da inda jama’a suke so su tafi, to a can ne za su tafi.
Game da rikicin cikin gida da PDP ke fama da shi, gwamnan ya ce yanzu an sasanta matsalolin.
Ya ce an yi zama na musamman da na haɗin kai domin kawar da bambance-bambancen da suka jawo rabuwar kawuna.
Ya ce kusan shekara guda suna fama da wannan rikicin, amma yanzu da yardar Allah an wuce wannan mataki.
Ya ce shugabanni da magoya bayan jam’iyyar sun yi farin ciki da zaman da aka yi, kuma suna fatan rikicin ya zama tarihi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Gwamna Muftwan Sauya Sheƙa
এছাড়াও পড়ুন:
Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
Ɗan Majalisar Tarayya mai Wakiltar Sabon Gari Daga Jihar Kaduna, Sadiq Ango Abdullahi, ya fice daga Jam’iyyarsa ta PDP.
Honorabul Abdullahi wanda shi ne Mataimakin Shugaban Kwamishinan Hukumar Kula da Hanyoyi (FERMA) ya alaƙanta ficewarsa da rikicin cikin gida da rabuwar kai da ya ki ci ya ƙi cinyewa a jam’iyyar.
A ranar Litinin ya aike da wasikar ta ficewa ga Shugaban PDP na Mazabar Hanwa da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, yana mai cewa rikicin ya hana shi taɓukawa matsayin zaɓaɓɓen ɗan Majalisar Tarayya.
Ya cewa saboda haka yana dacewar ficewarsa daga jam’iyyar ba tare da la’akari da siyasa ba, domin amfanin ɗauƙacin al’ummar mazabar.
Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjayeYa yaba wa jam’iyyar bisa damar da kuma gudummawar da ta ba shi domin hidimta wa al’umma.