HausaTv:
2025-11-27@22:36:09 GMT

Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya

Published: 2nd, July 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa hare-haren HKI da Amurka a yankin yammacin Asiya ya kara rashin zamn lafiya a yankin.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadin haka ne a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Girka a jiya talata .

Ya kuma kara da cewa hare-haren sun yu watsi da hanyar zaman lafiya da kuma zaman lumana a yankin. Ya kuma yi sanadiyyar karin tashe tashen hankula a yankin.

Ministan ya bukaci kasashen duniya gaba daya su yi tir da HKI da kuma Amurka wadanda suka keta hurumin kasa mamba a MDD ba tare da wani daloli nay an haka ba. Ya ce hare-haren da kasashen biyu suka kaiwa JMI wanda ya cinye rayukan mutane da dama ya sabawa kudurin MDD ta 2231, wanda hakan barazana ce ga zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa.

Ministan ya kara da cewa wadannan hare-hare sun zo ne a dai-dai lokacinda Iran da Amurka suna kan teburin tattaunawa don fahintar juna kan shirin Nukliyar kasar. Wanda haka yin watsi da hanyar diblomasiyya da kuma zaman lafiya ne.

Daga karshe ministan ya bayana cewa ayyukann ta’addanci wanda HKI take aikatawa a Gaza shi ne yake kunna wutan fitina a yankin da kuma duniya gaba daya.

A nashi bangren  ministan harkokin wajen kasar Girka ya ce, yana mika ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wadannan hare-hare sannan yana fatan tsagaita wutan da aka samu zai dore. Ya kuma nuna damuwarsa da abinda yake faruwa a gaza kan falasdinawa musamman rashin barin abinci ya shiga yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa

Gwamnonin jihohin  Arewa 19 za su gudanar da muhimmin taro a ranar Asabar, 29 ga Nuwamba, domin tattauna matsalolin tsaro da suka addabi yankin.

Mai bai wa Gwamnan Nasarawa shawara na musamman kan harkokin jama’a, Peter Ahemba, ne ya sanar cewa, taron gwamnonin Arewa da aka shirya a Kaduna zai samu halartar manyan sarakunan gargajiya.

“Manufar taron ita ce samar da matsaya ɗaya wajen fuskantar matsalolin tsaro da ke damun yankin, tare da tsara hanyar magance su,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, za a yanke muhimman shawarwari a taron domin tabbatar da tsaron yankin.

’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina

Ahemba ya bayyana cewa, sakamakon ƙalubalen tsaro da wasu jihohin Arewa ke fuskanta, gwamnatin Nasarawa ta ɗauki matakan gaggawa ta hanyar shirya taron tsaro na musamman, inda za a yanke shawarar da za ta kare jihar daga duk wata barazanar tsaro.

“Ya zama wajibi ga ’yan ƙasa su taka rawa wajen magance barazanar tsaro a ƙasarmu da jihohinmu. Don haka, dole ne jama’a su riƙa ba wa hukumomin tsaro bayanai kan mutanen da ke da halin aikata laifi,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa
  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin
  • Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya