HausaTv:
2025-08-17@11:18:33 GMT

Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya

Published: 2nd, July 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa hare-haren HKI da Amurka a yankin yammacin Asiya ya kara rashin zamn lafiya a yankin.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadin haka ne a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Girka a jiya talata .

Ya kuma kara da cewa hare-haren sun yu watsi da hanyar zaman lafiya da kuma zaman lumana a yankin. Ya kuma yi sanadiyyar karin tashe tashen hankula a yankin.

Ministan ya bukaci kasashen duniya gaba daya su yi tir da HKI da kuma Amurka wadanda suka keta hurumin kasa mamba a MDD ba tare da wani daloli nay an haka ba. Ya ce hare-haren da kasashen biyu suka kaiwa JMI wanda ya cinye rayukan mutane da dama ya sabawa kudurin MDD ta 2231, wanda hakan barazana ce ga zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa.

Ministan ya kara da cewa wadannan hare-hare sun zo ne a dai-dai lokacinda Iran da Amurka suna kan teburin tattaunawa don fahintar juna kan shirin Nukliyar kasar. Wanda haka yin watsi da hanyar diblomasiyya da kuma zaman lafiya ne.

Daga karshe ministan ya bayana cewa ayyukann ta’addanci wanda HKI take aikatawa a Gaza shi ne yake kunna wutan fitina a yankin da kuma duniya gaba daya.

A nashi bangren  ministan harkokin wajen kasar Girka ya ce, yana mika ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wadannan hare-hare sannan yana fatan tsagaita wutan da aka samu zai dore. Ya kuma nuna damuwarsa da abinda yake faruwa a gaza kan falasdinawa musamman rashin barin abinci ya shiga yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kama manyan shugabannin ’yan ta’addan ƙungiyar Ansaru — Ribadu

Jami’an tsaro sun kama manyan shugabannin ƙungiyar ’yan ta’adda ta Ansaru, ciki har da shugaban ƙungiyar, Mahmud Muhammad Usman wanda aka fi sani da Abu Baraa.

An daɗe ana zarginsa da kitsa hare-hare masu yawa a Najeriya.

’Yan sanda sun kama matashin da ya yi garkuwa da kansa a Ondo Majalisar dokokin Gombe ta fara duba ƙudirin ƙirƙirar sabbin gundumomi 13

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ne, ya tabbatar da kamen a wani taron manema labarai da ya gudanar a Abuja, a ranar Asabar.

Ya bayyana cewa an cafke Abu Baraa a watan Yuli bayan shafe tsawon watanni ana bin diddiginsa.

Haka kuma an kama wani shugaban ƙungiyar, mai suna Abubakar Abba.

Ribadu, ya ce wannan nasara babban ci gaba ne a yaƙi da ƙungiyar Ansaru, wacce ta ɓalle daga tsagin Boko Haram a shekarar 2012.

Duk da cewa a farko ta bayyana kanta a matsayin “ƙungiya mai tausayin jama’a” daga baya ta zama mai aikata mummunan ayyukan ta’addanci.

Ta kai wa sojoji, fararen hula da kuma gine-ginen gwamnati hare-hare.

Tsawon shekaru, ƙungiyar ta samar wa kanta maɓoya a cikin birane da kuma dazuka, musamman a kusa da yankin Kainji da ke tsakanin Jihohin Neja da Kwara har zuwa Jamhuriyar Benin.

A cewar Ribadu, Abu Baraa shi ne ke da alhakin shirya ayyukan ta’addanci a sassan Najeriya da kuma sace mutane da fashi don samun kuɗaɗen da suke amfani da su wajen aikata ta’addanci.

Mataimakinsa, Mahmud al-Nigeri wanda aka fi sani da Mallam Mahmuda, ya samu horo a ƙasar Libya tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015, inda ya ƙware wajen amfani da makamai da kuma haɗa bama-bamai.

Ribadu, ya danganta su da wasu manyan laifuka da suka haɗa da ɓalle gidan yarin Kuje a 2022, da harin da suka kai wajen haƙar ‘uranium’ a Jamhuriyar Nijar.

Har ila yau, suna da hannu a sace injiniyan Faransa Francis Collomp a 2013, da kuma sace manyan mutane kamar Alhaji Musa Umar Uba na Daura a 2019 da Sarkin Wawa na Jihar Neja.

Ribadu, ya ce wannan kamen babban nasara ce a ƙoƙarin Najeriya na kawar da ta’addanci.

Ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun samu muhimman bayanai daga hannunsu, kuma ana bincike a kansu domin kawo ƙarshen ƙungiyar.

Ya jinjina wa dakarun soja da sauran hukumomin tsaro bisa jajircewarsu, inda ya bayyana wannan babban ci gaba ne wajen rushe ƙungiyar Ansaru gaba ɗaya.

Ministan Watsa Labarai, Mohammed Idris, ya roƙi ’yan Najeriya da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani domin kawo ƙarshen ta’addanci, tare da tabbatar da tsaro da ci gaban tattalin arziƙi.

Wannan nasara na zuwa ne bayan shekara tara da kama wani tsohon shugaban Ansaru, Khalid al-Barnawi, a shekarar 2016.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza: A cikin sa’o’i 24 Mutane da dama sun yi shahada daruruwa sun jikkata a hare-haren Isra’ila
  • An kama manyan shugabannin ’yan ta’addan ƙungiyar Ansaru — Ribadu
  • Aragchi: Yiyuwan Sake Shiga Yaki Da HKI Nan Kusa Yana Da Wuya
  • Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar
  • Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Koka Kan Hana Shigar Da Kayayyakin Jin Kai Yankin Gaza
  • Za’a Fara tattaunawar Kasa Dangane Da Talauci da Kuma Rashin Adalci A Rabin Arziki A kasar
  • Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
  • Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
  • Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9
  • Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ