Gwamnatin kasar Iran ta gargadi kasashen yammacin Asiya kan cewa mai yuwa yaki ya sake barkewa tsakaninta da HKI, akwai tababa kan cewa HKI zata kiyaye budewa juna wuta da ta cimma da kasar Iran.

Shafin yanar gizo na labarai ArabNews na kasar Saudiya ya nakalto Manjo Janar Abdulrahman Musawi babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran  yana fadar haka a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da ministan tsaro na kasar Saudiya Yerima Khalid bin Salman, ya kuma kara da cewa HKI ba kasashe abin amincewa ba.

Musawi ya ce sojojin JMI a shirye suka su dakile dukkan hare-haren da HKI zata kawo nan gaba.

A wani bangare kuma shugaban hukumar makamashin nukliya ta kasa da kasa ta kuma MDD IAEA yace Iran tana iya sake fara aikin tace makamashin Uranium a cikin watanni masu zuwa . Rafael Grossi ya bayyanawa tashar talabijin ta CBS a ranar Lahadi kan cewa , bayana hare-haren Amurka kan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar Iran ba zamu iya cewa kome yak are kuma. Saboda ba wanda ya isa y araba kasar Iran daga fasahar nukliyar da take da shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Har ila yau, Maishaddar ya ci gaba da bayyana cewa; dangane da batun da mutane ke yi na cewa, alaka tsakaninsa da jarumi kuma mawaki Umar M. Sharif ta yi tsami, duba da cewa; an daina ganinsa a ci gaban shirin ‘Gidan Sarauta’ da Maishadda ke daukar nauyi, Bashir ya bayyana cewa; wannan magana ko kusa babu kamshin gaskiya a ciki, don ba a ga Umar a shirin ‘Gidan Sarauta’ zango na 4 ba, wannan ba dalili ne da zai sa a yi tunanin ko akwai wata matsala a tsakanina da shi ba, domin kuwa; a duk wani shiri mai dogon zango, akwai lokacin da za a daina ganin jarumi, amma kuma daga baya ya sake bayyana.

Bashir ya kara da cewa, yanzu kamar yadda ake daukar fim din ‘Alakata da Nana Firdausi’, har wasu ma ke tunanin ko akwai maganar aure a tsakaninmu, duk da dai Allah ne ke yi; saboda yanzu haka, matata ’yar fim ce. Don haka, zuwa yanzu dai babu wani batu na aure tsakanina da Nana, kawai dai muna da fahimtar juna tsakaninmu, sannan kuma na yi amanna da yanayin aikinta, saboda duk wani aiki da za mu yi tare da ita; ina yaba aikin nata kwarai da gaske, saboda yadda ta ke mayar da hankali wajen ganin ta yi abin da ya dace, musamman ma aikin kamfanina.

Lokacin da yake amsa tambaya a kan burin da yake da shi a wannan masana’anta, Bashir ya ce; babu wani burin da yake da shi a yanzu da ya wuce a ce watarana ya dauki nauyin fim a wata kasa daban, ba Nijeriya ba; musamman Kasar Indiya. 

“Burina yanzu a Masana’antar Kannywood, bai wuce ganin na zama ‘International Furodusa’ ba, wato ya kasance ina yin fina-finai ba a iya nan gida Nijeriya ba, har ma da kasashen duniya; musamman ma Kasar Indiya”, in ji shi.

“Domin kuwa, in dai ana iya yin fim a samu riba a Kasar Indiya, to ni ma ina fatan watarana a ce nayi, hakan ya sa tun a yanzu na fara gayyato wasu daga cikin jaruman da ba Arewacin Nijeriya suke aiki ba, kamar irin su Kanayo O. Kanayo da sauran makamantansu; domin su zo su taya ni aiki. Burin da nake da shi ga wannan masana’anta mai albarka, ba zai fadu ba; domin idan da zan samu dama, zan yi abin da zai sa Kannywood ta shiga duniya kowa da kowa ya santa”. 

Ya ci gaba da cewa, harkar fim; ba karamar harka ba ce a idon duniya, kamar yadda wasu ke tunani. Dalili kuwa shi ne, a fim ne za ka samu daukaka, kudi da kuma masoya, sannan kuma a nan ne za ka bugi kirjin cewa; an san fuskarka, haka zalika an san sunanka, har inda ba ka yi tsammani ba, kuma a harkar fim ne kadai za ka taka kafarka inda ba ka taba tsammanin cewa; za ka iya takawa ba, misali a Nijeriya, duk inda gwamna ke tunanin an san shi, haka nan dan fim ma zai yi wannan tunani, domin kuwa ta hanyar fim sunansa ya zaga ko’ina.

A karshe, Bashir Abubakar Maishadda, wanda ake yi wa lakabi da ‘King Of Bod Office’, ya yi kira ga mutane da su daina raina mutum a duk inda suka gan shi, domin kuwa ba su san abin da zai zama a nan gaba ba, har ma ya yi misali da kansa, inda ya ce a farkon lokacin da ya shigo masana’antar, mutane da dama sun sha tsangwamar sa tare da toshe wasu hanyoyin da suke tunanin zai iya koyon wani abu, amma kuma yanzu da Allah ya mayar da shi abin da ya zama, sai suke mamaki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
  •  Iran: Babu Wani Alfanu A Ci Gaba Da Bai Wa IAEA Hadin Kai
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Da Isra’ila Kanta
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Jaddada Cewa: Iran Tana Da Hakkin Tace Sinadarin Uranium A Kasarta
  • Darakta Janar Na Hukumar IAEA Ya Ce; Babu Tabbas Iran Na Da Shirin Mallakar Makamin Nukiliya
  • Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD