Nijeriya ce kasa ta 12 mafi talauci a duniya — IMF
Published: 29th, June 2025 GMT
Wani sabon rahoto da Asusun Bayar da Lamuni IMF ya fitar ya ce Nijeriya na mataki na 12 a cikin jerin kasashe mafiya talauci a fadin duniya.
IMF ya ce talauci na kara karuwa a cikin kasar da ta dauki shekaru biyu tana kokarin sauya fuskar tattalin arziki, amma kuma take dada fadawa cikin duhu na tattalin arziki.
Jaridar Cable ta ruwaito cewa, Nijeriya tana mataki na 12 a cikin kasashe mafiya talauci bisa la’akari da karfin tattalin arziki a ma’aunin GDP na Dalar Amurka 807 a bana.
Kawo yanzu dai shekaru biyu bayan kaddamar da jerin sauye-sauye ga tattalin arziki, amma daga dukkan alamu Nijerya na dada fadawa cikin matsalar talauci idan aka yi la’akari da kasashe 189 da IMF ya gudanar da bincike a cikinsu.
A cikin kasashe 189 da aka gudanar da bincike a cikinsu, Najeriyar na a mataki na 178, inda ta zarta kasashe irin su Yemen da Sudan ta Kudu da Kwango da Nijar da Sudan, wadanda kusan dukkaninsu ke fama da rigingimu a halin yanzu.
Ana kallon sabon rahoton a matsayin alamun kasawa a bangare na masu mulkin Nijeriya da ke fadin cewar suna da burin ceto kasar da ke kara samun nakasu, kamar yadda Ibrahim Shehu, sakataren kungiyar inganta tattalin arzikin arewacin Najeriya ya bayyana.
Akalla Naira tiriliyan 21 ne ake jin matakan gwamnatin kasar guda uku sun samu daga zare tallafin man fetur a shekaru guda biyu.
Ko bayan wasu Naira Tiriliyan 96 da masu mulkin na Abuja suka karba da sunan bashi, akwai Naira tiriliyan guda a shekara da masu mulkin ke samu sakamakon ragin tallafi bisa kudin wuta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nijeriya tattalin arziki
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
Jiya Laraba 25 ga watan Yuni ne, a birnin Rome na kasar Italiya, aka kaddamar da gagarumin bikin nune-nunen kayan al’adu na murnar cika shekaru 55 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Italiya, karkashin hadin-gwiwar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, da ma’aikatar raya al’adu ta Italiya, da gidan adana kayan tarihi na wayin kan dan Adam na Italiya, da cibiyar koyon fasahohin zane-zane dake birnin Rome na Italiya, da kungiyar wasan kwallon kafar Italiya da sauransu.
Bikin na nuna nagartattun kayayyakin al’adu sama da dari biyu da shahararrun masu zane-zane, da magadan al’adun gargajiya da ba na kayayyaki ba, da sauran wasu masu aikin fasahohin al’adu na kasar Sin fiye da 100 suka yi, tare da kayayyakin al’adu masu daraja sama da 100 da aka adana a gidan adana kayan tarihi na wayin kan dan Adam na Italiya.
A wannan rana kuma, CMG ya shirya bikin musanyar al’adu na murnar cika shekaru 55 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Italiya a birnin Rome, inda aka kaddamar da “makon nuna fina-finan kasar Sin na shekara ta 2025 a Italiya”. (Murala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp