Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos
Published: 2nd, July 2025 GMT
Babbar Kotun Jihar Filato da ke zamanta a Jos, ta yanke wa dalibin nan na makarantar GSTC Bukuru, Odey Emmanuel, hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kashe malamin makarantarsu a kan abinci.
Alkalin kotun, Mai Shari’a S.J. Bakfur, ya ce an sami Odey ne da laifin na kisan kai wanda kotun ta ce ya saba da tanade-tanaden sassa na 188 na 189 na kundin dokar manyan laifuffuka ta jihar Filato ta shekara ta 2017.
A cewar alkalin, masu shigar da kara sun gabatar da hujjojin da suka iya gamsar da kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin da aka zarge shi da aikatawa.
Babban lauyan gwamnatin jihar kuma Kwamishinan Shari’a, Philemon Audu Daffi ne ya jagoranci lauyoyi masu gabatar da kara.
Lamarin dai ya faru ne ranar 30 ga watan Yulin 2022, a cikin harabar makarantar da ke karamar hukumar Jos ta Kudu.
Lauyoyin sun shaida wa kotun cewa dalibin ya kasha malamin ne mai suna Job Dashe a dakin girkin makarantyar lokacin da ake rabon abinci ga dalibai.
Sun ce a lokacin ne malamin a hukunta dalibin bisa zargin ya karbi kason abinci har sau biyu, inda dalibai suka tabbatar da haka, lamarin da ya harzuka dalibin.
Daga nan ne dalibin ya dauko wuka ya daba wa malamin a kahon zuciya, nan take aka garzaya da shi asibiti amma kafin a je y ace ga garinku nan.
Sai dai ko da a aka karanta masa laifin da aka zarge shi da aikatawa a kotun, dalibin bai musa ba.
Da yake yanke hukuncin, Alkalin kotun ya jaddada cewa kisan malami a makaranta babbar barazana ce ga al’umma da ya zama wajibi a dauki tsattsauran mataki a kai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rataya
এছাড়াও পড়ুন:
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Shugabannin masana’antu sun kuma yi kira ga gwamnati da ta daidaita tattalin arziki, inganta saukin gudanar da harkokin kasuwanci, da aiwatar da shirye-shiryen tallafi ga masana’antu na cikin gida.
Bugu da kari, masana sun nuna cewa rikicin kudin waje da rashin daidaito a kimar musayar kudi su ne manyan matsaloli ga kamfanoni masu zaman kansu daga kasashen waje, inda kalubalen samun damar mayar da ribar kamfani zuwa kasashen waje da samun kudin waje ke rage amincewar masu zuba jari sosai kuma yana karfafa su su bar kasar.
Binciken da LEADERSHIP Sunday ta gudanar ya nuna cewa yanayin tattalin arzikin Nijeriya ya sha wahala tun daga shekarar 2020, inda wasu kamfanoni suka rufe ayyukansu, ko suka yi kaura, ko kuma suka rage yawan ayyukansu a kasar.
Ana danganta wannan yanayi da wahalhalun tattalin arziki, canje-canjen kimar kudi, da tsadar gudanar da ayyuka, wanda hakan ya haifar da asarar ayyukan yi da kuma rashin daidaiton tattalin arziki mai yawa.
Wasu daga cikin manyan kamfanonin da suka bar Nijeriya sun hada da Standard Biscuits Nigeria Limited, NASCO Fiber Product Limited, Union Trading Company Nigeria Plc, da Deli Foods Nigeria Limited.
Ficewar wadannan kamfanonin daga kasuwar Nijeriya ya samo asali ne daga tasirin rashin daidaiton tattalin arziki da sauran kalubalen gudanarwa.
Yawancin kamfanonin sun bayyana cewa matsalolin tattalin arziki masu tsanani, canje-canjen kimar kudi marasa tabbas, da hauhawar farashin gudanar da ayyuka su ne manyan dalilan da suka sa suka yanke wannan shawara.
“Nijeriya dole ne ta samar da tsarin da zai ja hankalin wadanda za su zuba jari a masana’antu, hakar ma’adanai, wadanda za su sarrafa albarkatun kasa da kayan albarkatun da ake da su, tare da tabbatar da ci gaban tattalin arziki mai hadin kai,” in ji shi.
Haka kuma, shugaban Kungiyar Masu Kananan Harkokin Kasuwanci na Nijeriya (ASBON), Dakta Femi Egbesola, ya bayyana cewa ficewar kamfanoni masu zaman kansu na kasashen waje ya shafi yawancin Kananan da Matsakaitan Harkokin Kasuwanci (SMEs) da kamfanoni na cikin gida da ke aiki a kasar, tare da karawa da cewa gwamnati dole ne ta dauki matakan gaggawa don hana ficewar kamfanonin ketare.
A yayin da yake magana da daya daga cikin wakilanmu, Daraktan Gudanarwa na Cowry Asset Management Company, Johnson Chukwu, ya bayyana cewa haduwar rikicin kudin waje da rashin daidaito a kimar musayar kudi ya yi tasiri mara kyau ga ra’ayin masu zuba jari na kasashen waje wajen ci gaba da shiga harkokin zuba jari na kamfanoni masu zaman kansu a kasar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA