Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos
Published: 2nd, July 2025 GMT
Babbar Kotun Jihar Filato da ke zamanta a Jos, ta yanke wa dalibin nan na makarantar GSTC Bukuru, Odey Emmanuel, hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kashe malamin makarantarsu a kan abinci.
Alkalin kotun, Mai Shari’a S.J. Bakfur, ya ce an sami Odey ne da laifin na kisan kai wanda kotun ta ce ya saba da tanade-tanaden sassa na 188 na 189 na kundin dokar manyan laifuffuka ta jihar Filato ta shekara ta 2017.
A cewar alkalin, masu shigar da kara sun gabatar da hujjojin da suka iya gamsar da kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin da aka zarge shi da aikatawa.
Babban lauyan gwamnatin jihar kuma Kwamishinan Shari’a, Philemon Audu Daffi ne ya jagoranci lauyoyi masu gabatar da kara.
Lamarin dai ya faru ne ranar 30 ga watan Yulin 2022, a cikin harabar makarantar da ke karamar hukumar Jos ta Kudu.
Lauyoyin sun shaida wa kotun cewa dalibin ya kasha malamin ne mai suna Job Dashe a dakin girkin makarantyar lokacin da ake rabon abinci ga dalibai.
Sun ce a lokacin ne malamin a hukunta dalibin bisa zargin ya karbi kason abinci har sau biyu, inda dalibai suka tabbatar da haka, lamarin da ya harzuka dalibin.
Daga nan ne dalibin ya dauko wuka ya daba wa malamin a kahon zuciya, nan take aka garzaya da shi asibiti amma kafin a je y ace ga garinku nan.
Sai dai ko da a aka karanta masa laifin da aka zarge shi da aikatawa a kotun, dalibin bai musa ba.
Da yake yanke hukuncin, Alkalin kotun ya jaddada cewa kisan malami a makaranta babbar barazana ce ga al’umma da ya zama wajibi a dauki tsattsauran mataki a kai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rataya
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Ya samu munanan raunuka a harin da aka kai masa, wanda daga baya ya mutu.
Janar Kangye ya ƙara da cewa Danbokolo ya fi Bello Turji tsabibanci, shi ne ya jagoranci harin watan Disamban 2021 a ƙaramar hukumar Shinkafi ta Jihar Zamfara, inda ya ƙone fasinjoji da ransu a cikin mota.
Hakazalika, ya bayyana cewa Danbokolo na amfani da wata ƙwaya mai suna ‘pentazocine’ domin ci gaba da aikata miyagun laifuka.
Yanzu haka, sojojin Operation FASAN YAMA suna ci gaba da neman Bello Turji wanda ya ɓuya.
Janar Kangye ya tabbatar da cewa rundunar sojin Nijeriya tana da ƙwarin gwiwar samar da zaman lafiya a dukkanin sassan ƙasar nan.
Ya kuma roƙi haɗin kan ‘yan Nijeriya don cimma wannan buri.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp