Aminiya:
2025-11-27@21:48:28 GMT

Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos

Published: 2nd, July 2025 GMT

Babbar Kotun Jihar Filato da ke zamanta a Jos, ta yanke wa dalibin nan na makarantar GSTC Bukuru, Odey Emmanuel, hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kashe malamin makarantarsu a kan abinci.

Alkalin kotun, Mai Shari’a S.J. Bakfur, ya ce an sami Odey ne da laifin na kisan kai wanda kotun ta ce ya saba da tanade-tanaden sassa na 188 na 189 na kundin dokar manyan laifuffuka ta jihar Filato ta shekara ta 2017.

Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu

A cewar alkalin, masu shigar da kara sun gabatar da hujjojin da suka iya gamsar da kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin da aka zarge shi da aikatawa.

Babban lauyan gwamnatin jihar kuma Kwamishinan Shari’a, Philemon Audu Daffi ne ya jagoranci lauyoyi masu gabatar da kara.

Lamarin dai ya faru ne ranar 30 ga watan Yulin 2022, a cikin harabar makarantar da ke karamar hukumar Jos ta Kudu.

Lauyoyin sun shaida wa kotun cewa dalibin ya kasha malamin ne mai suna Job Dashe a dakin girkin makarantyar lokacin da ake rabon abinci ga dalibai.

Sun ce a lokacin ne malamin a hukunta dalibin bisa zargin ya karbi kason abinci har sau biyu, inda dalibai suka tabbatar da haka, lamarin da ya harzuka dalibin.

Daga nan ne dalibin ya dauko wuka ya daba wa malamin a kahon zuciya, nan take aka garzaya da shi asibiti amma kafin a je y ace ga garinku nan.

Sai dai ko da a aka karanta masa laifin da aka zarge shi da aikatawa a kotun, dalibin bai musa ba.

Da yake yanke hukuncin, Alkalin kotun ya jaddada cewa kisan malami a makaranta babbar barazana ce ga al’umma da ya zama wajibi a dauki tsattsauran mataki a kai.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rataya

এছাড়াও পড়ুন:

Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa

Fitaccen malamin addinin Musulunci nan daga Jihar Bauchi, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya rasu.

Ɗansa, Sayyadi Ali Dahiru Usman Bauchi ne,  ya tabbatar wa Aminiya rasuwar malamin.

Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka

Ya ce sun karɓi wannan ƙaddara tare da gode wa Allah bisa rayuwar da malamin ya yi.

“Tabbas Sheikh ya koma ga Mahaliccinsa. Daga Allah muke, kuma gare Shi za mu koma,” in ji Sayyadi.

“Lokacin Sheikh ya yi. Mun gode wa Allah Maɗaukaki. Ya bai wa Sheikh tsawon rai, kuma rayuwarsa ta yi kyau. Alhamdulillah,” in ji shi.

Sayyadi, ya ce zuwa yanzu ba su yanke inda za a yi jana’izar malamin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Sheikh Dahiru Bauchi: Malamin da zuri’arsa ta fi kowacce yawan mahaddata Alkur’ani
  • Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa
  • ’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa
  • NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta
  • Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza