Aminiya:
2025-06-30@01:21:02 GMT

Mangal ya bayar tallafin N80m don yi wa marasa lafiya tiyata a Katsina

Published: 30th, June 2025 GMT

Fitaccen ɗan kasuwar nan, Alhaji Dahiru Bara’u Mangal, ya bayar da tallafin Naira miliyan 80 don taimaka wa mutane masu fama da cutar mafitsara da matsalar gwaiwa domin yi musu tiyata kyauta.

An gudanar da tantance marasa lafiyar a Asibitin Ƙashi na Amadi Rimi kafin a fara aikin tiyatar a ranar Asabar da ta gabata.

Kebbi: PDP za ta yi haɗaka don ƙalubalantar APC a zaɓen 2027 Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello Turji

Alhaji Kabir Husaini, wanda ke jagorantar aikin, ya bayyana cewa wannan shi ne karo na uku da Mangal ke bayar da irin wannan taimako ga marasa lafiya masu ƙaramin ƙarfi.

Ya ce a baya, Mangal ya taimaka wajen yi wa masu lalurar gwaiwa tiyata.

Tun bayan fara shirin a shekarun baya, sama da mutum 3,000 ne suka ci gajiyar aikin tiyatar da aka gudanar a wurare daban-daban.

A wannan karon, Mangal ya bayar da Naira miliyan 20 daga cikin tallafin domin yi wa mutum 100 tiyata a kan cutar mafitsara da kuma lalurar gwaiwa.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Adamu Aliyu, ya ce da babu wannan tallafi, da har yanzu yana fama da cutar saboda ba shi da isasshen kuɗi don biyan kuɗin tiyatar.

Alhaji Mangal ya fara bayar da irin wannan taimako tun shekarar 2016, kuma tallafin yana zuwa har wasu maƙwabtan jihohi da ma Jamhuriyar Nijar.

Wata mata da ta nemi a sakaya sunanta ta ce wannan aiki ya zama darasi ga masu hali da ba sa son taimakon jama’a.

“Tun sama da shekara 20 Alhaji Mangal ke ciyar da marasa ƙarfi da abinci, kuma har yanzu bai fasa ba,” in ji ta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Cutar Mafitsara Gwaiwa Marasa Lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Zazzau ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin aure da aka kashe a Jihar Filato.

Tun da farko, Hakimin Basawa, Haruna Abubakar ne, ya wakilci Sarkin lokacin da lamarin ya faru, saboda Sarkin ya yi tafiya.

Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC

Sarkin, ya bayyana baƙin cikinsa bisa wannan mummunan lamari, inda ya roƙi iyalan da su ɗauki wannan a matsayin ƙaddara.

Ya yaba da yadda suka yi haƙuri kuma suka bar komai ga hukuma, ba tare da ɗaukae doka a hannunsu ba.

Sarkin ya kuma tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kaduna na ƙoƙarin ganin an bi wa waɗanda abin ya shafa haƙƙinsu.

Ya ƙara da cewa zaman lafiya da haƙuri su ne mafita ga duk wata matsala, kuma hakan zai kawo ci gaba a tsakanin al’umma.

A yayin ziyarar, Sarkin ya samu rakiyar wasu daga cikin ’yan majalisarsa da hakimai.

Ya sake roƙon jama’a da su ci gaba da zaman lafiya tare da miƙa lamarin ga Allah.

Da yake magana a madadin iyalan garin, Mallam Muhammadu Dan Bami, ya gode wa Sarkin bisa ziyarar da ya kawo, tare da bayyana cewa mutanen garin masu bin doka da son zaman lafiya ne.

Daga ƙarshe, ya roƙi Sarkin da ya taimaka wajen ganin gwamnati ta cika alƙawarin da ta ɗauka na bi masu haƙƙinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mangal ya bada tallafin N80m don yi wa marasa lafiya tiyata a Katsina
  • Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
  • Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
  • Har yanzu mun gaza gano dalilin ɓullar COVID-19 — WHO
  • Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku
  • Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi
  • Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
  • Sarkin Zazzau ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
  • 2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya