HausaTv:
2025-10-13@18:05:28 GMT

HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin

Published: 30th, June 2025 GMT

Sojojin HKI sun kai falasdinawa akalla 72 ga shahada a safiyar yau Litinin, daga cikinsu har da yara kanana da kuma wadanda suke jiraran a basu taimakon abinci a cibiyoyinsu a cikin Gazzar.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a yau litinin a Gaza sojojin HKI sun kashe Falasdinawa a wurare da dama a gaza.

Labarin ya kara da cewa an garzaya da wadanda suka ji ciwo zuwa asbitin Al-Ahli. Bayan haka yahudawan kai kai hare-hare a yankin Zaitun da kuma kasuwar zawiyya.

Labarin ya kara da cewa baba gadaje a Asbitin don haka zaka ga wadanda suka ji ciwon kwance a kasa. Har’ila yau labaran sun bayyana cewa mafi yawan wadanda sojojin yahudawa suka kashe sun kashesu ne a cibiyar bada agajin gaggawa wanda Amurka da HKI suka tsara don kashe mafi yawan adadi da zasu iya kashewa a Gaza, bayan sun hanasu abinci na kimani watanni 3.

A karshen watan mayun de ya gabata ne Amurka tare da yahudawan suka bullo da wannan tarkon don kara kashe Falasdinawa bayan sun hana shigo da abinci yankin.  Suna kashesu ne a dai-dai lokacinda suke cikin tsananin yunwa. Inda ya zama masu dole su je su nemi abinci duk inda yake.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi 

’Yan bindiga sun kashe sojojin Nigeriya guda uku a wani kwanton ɓauna da suka yi masu a lokacin da suke ƙoƙarin hana yin garkuwa da wasu mutane a ƙauyukan ƙananan hukumomin Sakaba da Danko-Wasagu a Jihar Kebbi.

Sojojin da aka kashe an yi masu sutura a babban barikin sojoji da ke garin Zuru, hedikwatar ƙaramar hukumar Zuru.

Mai Martaba Sarkin Zuru Alhaji Sanusi Mika’ilu Sami, ya halarci janazar domin tausayawa da jinjina wa marigayin kan sadaukarwar da suka yi a wurin kare mutanen ƙasa.

Majiyar da ta shaida wa Aminiya ta ce sojojin sun kai ɗauki ne a lokacin da suka samu labarin ’yan ta’addan sun kai farmaki tare da ƙoƙarin yin garkuwa da mutane don neman kuɗin fansa.

Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina ’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali — Likita

Sai dai ana jiran bayani daga rundunar soja ta kasa kan wadannan jami’ai nata da aka kashe a fagen daga a yakin jihar Kebbi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza
  • Falasdinawa Sun Gano Gawakin Wadanda HKI Ta Kashe A gaza  Fiye Da 320 Cikin Kwanaki Biyu Kacal
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta
  • ’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi