Jaridun kasar Amurka sun bayyana cewa; Isra’ila ta kasa cimma manufofin da ta ayyana a yaki da Iran, sannan kuma ta kara zama saniyar ware a duniya.

Mujallar “Foreign Policy” ta yi ishara da sakamakon yakin da take cewa, ya zamarwa Amurka da kawarta   Isra’ila juyewar reshe da mujiya,domin harin da su ka kai wa Shirin Iran na Nukiliya bai iya kawo karshensa baki daya,maimakon haka ma sai ya jazawa Tel Aviv asarar mai yawa da kuma karfafa kishin kasa a tsakanin Iraniyawa.

Har ila yau, rahoton mujallar ta “”Foreign Policy” ya ci gaba da cewa; Asarar da aka yi a Isra’ila, tana firgitarwa”,amma a cikin Iran babu cikakken bayani akan girman barnar da aka yi- da hakan yake a  matsayin tsaka mai yuwa ta fuskar muhimman manufofin da Isra’ilan ta so cimmawa da kuma kawarta Amurka.”

Bugu da kari mujallar ta “Foreign Policy” ta ce; Babu wanda yake gaskata abinda Isra’ila take fada na cewa ta rusa Shirin makamashin Nukiliyar Iran,domin hukumomin leken asiri na turai suna cewa, dukkanin sanadarorin kera makaman Nukiliya suna nan kalau ba abinda ya same su.”

Wani sashe na rahoton ya ce; HKI ba ta iya samar da kandagarko na Nukiliya a yakinta da Iran ba,maimakon hakan ma, abu ne mai yiyuwa harin da Isra’ilan da Amurka su ka kai wa Iran ya ba ta karfin gwiwar yin tunanin samar da makamin Nukiliya” a fadar wannan mujalla.

Iran dai ta sha bayyana cewa; Shirinta na sulhu ne, ba kuma wanda yake da hakkin hana ta cin moriyar alfanu mai yawa dake cikin fasahar makamashin Nukiliya.  

Rahoton ya kuma ce; gwamnatin Amurka ta fake da dalilai na karya wajen kai wa Iran hari.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza

An gano gawar wani jami’in sojin gwamnatin mamayar Isra’ila da ya kashe kansa bayan yaki a Gaza

Rundunar sojin Isra’ila ta sanar da gano gawar wani jami’in sojin gwamnatin mamayar Isra’ila a wani dajin da ke arewacin Isra’ila. Sojan ya kashe kansa ne a lokacin da yake aikin soja, wanda ya kawo adadin sojojin da suka kashe kansu tun farkon wannan shekara zuwa 18, kamar yadda kafafen yada labaran haramtacciyar kasar Isra’ila suka bayyana.

Gidan rediyon sojojin mamayar Isra’ila ya bayyana cewa: Rundunar sojin ta bude bincike kan lamarin, tare da bayyana cewa jami’in da ya kashe kansa yana shiyya ta 99 da ke yaki a zirin Gaza.

Jaridar Yedioth Ahronoth ya watsa rahoton cewa: Jami’in dan shekaru 28 ya shiga yakin da ake yi a zirin Gaza ne a makonnin da suka gabata.

Wani bincike da sojojin mamayar Isra’ila suka gudanar, wanda aka buga sakamakonsa a ranar 3 ga watan Agusta, ya nuna cewa mafi yawan wadanda suka kashe kansu a cikin dakarunta, sun faru ne sakamakon yanayin fada a zirin Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gwamnatin Mali Ta Bankado Wata Makarkashiyar Janyo Hargitsi A Kasar Tare Da Wargaza Shi August 15, 2025 Iran: Suna Bukatar Kawo Karshen Makaman Nukiliya Da Kuma Furuci Maras Daɗin Ji August 15, 2025 Kungiyar Ansarullahi Ta Kasar Yemen Ya Ce; Yahudawan Sahayoniyya Suna Yakar Al’ummar Falasdinu Duka Ne August 15, 2025 Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Koka Kan Hana Shigar Da Kayayyakin Jin Kai Yankin Gaza August 15, 2025 Laifukan Cin Zarafi Musamman Kisha Kiyashi A Kasar Siyasa Ya Doshi Laifukan Yaki August 15, 2025 Kungiyar Ba Da Agaji Ta Sanar Da Yadda Cutar Kwalara Take Lashe Rayukan Mutane A Kasar Sudan August 15, 2025 Miliyoyin Mutane Sun Taru A Karbala Don Juyayin 40 Na Shahadarsa Imam Hussain(a) August 14, 2025 Sayyid Huthi Ya Yi gargadi Yiyuwar Tarwatsewar kasashen yankin idan HKI Ta  Tabbaga Shirinta August 14, 2025 An Bukaci Ficewar Marasa Lafiya da Likitoci daga Wani Babban Asbiti A birnin London August 14, 2025 Za’a Fara tattaunawar Kasa Dangane Da Talauci da Kuma Rashin Adalci A Rabin Arziki A kasar August 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Ta Jefa Boma-Bomai Kan Tashar Samar Da Wutan Lantarki A Yemen
  • APC ta lashe zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsanyawa a Kano
  • Denmark na nazarin kakaba wa Isra’ila takunkumi kan batun Gaza
  • Jami’in Harkokin Shari’ar Kasa Da Kasa Na Iran Ya Yi Tofin Allah Tsine Kan Furucin Jami’ar Shari’ar Kasa Da Kasa
  • Takht-Ravanchi: Iran a shirye take ta ci gaba da tattaunawa kan hakkinta na nukiliya
  • Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu
  • Kungiyar Kare Hakkin Bil’Adama Ta Human Rights Watch Ta Ce; Kai Hari Kan Gidan Yarin Evin Na Iran Laifin Yaki Ne
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza
  • Iran: Suna Bukatar Kawo Karshen Makaman Nukiliya Da Kuma Furuci Maras Daɗin Ji