’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3
Published: 14th, March 2025 GMT
’Yan bindiga sun kai hari tare da tarwatsa mazauna ƙauyuka biyar da ke Karamar Hukumar Kachia a Jihar Kaduna.
Ƙauyukan da abin ya shafa sun haɗa da Unguwan Tauka, Unguwan Lalle, Sonudazuwa, Tsauni Dodo, da Dandauka.
Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu — ObasanjoWani jagoran al’umma ya tabbatar da faruwar harin, inda ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun kuma kai farmaki sansanin Fulani da ke Kubuwo, inda suka sace matasan makiyaya uku.
Sun kai harin ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 6 na yamma.
Shaidu sun bayyana cewa ’yan bindigar sun isa ƙauyukan suna harbe-harbe, lamarin da ya tilasta wa mazauna ƙauyukan tserewa.
“’Yan bindigar sun shigo suna harbi ta ko ina. Mutane suka riƙa gudu don tsira da rayukansu,” in ji wani jagora.
“Sannan sun sace matasa uku a sansanin Fulani, suka tafi da su cikin daji.”
Wani jami’in tsaro ya bayyana cewa ’yan bindigar sun tserewa wani farmaki da sojoji suka kai musu a dajin Kurutu-Azara, wanda ke iyaka da Ƙaramar Hukumar Kagarko.
Ya ce a kan hanyarsu ta tserewa ne, suka farmaki ƙauyukan da ke hanyarsu.
A yayin harin, ’yan bindigar sun ƙone mota da babur a Unguwan Tauka.
Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa, “An ƙone wa wani mutum mota sabuwa da ya sayo a Kaduna. Yana kan hanyar shigowa garin ne sai ya hango ’yan bindigar.
“Nan take ya fice daga motar ya tsere, suna ganin motar suma cinna mata wuta suka ƙone motar da wani babur.”
Wani ɗan banga daga cikin ƙauyukan da aka kai wa harin ya tabbatar da cewa jami’an tsaro na ci gaba da bin sahun ’yan bindigar.
Rundunar ’yan sandan yankin ta tabbatar da harin, amma ta ce za a tuntuɓi hedikwatar ’yan sandan m Kaduna don ƙarin bayani.
Sai dai kakakin rundunar, ASP Hassan Mansur, bai samu damar yin tsokaci kan harin ba lokacin da aka nemi jin ta bakinsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa hari Ƙauyuka Ƙonewa yan bindigar sun bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar amfani da ƙarfin soji kan Najeriya matuƙar gwamnatin ƙasar ba ta dakatar da kisan da ’yan ta’adda masu iƙirarin jihadi ke yi wa Kiristoci ba.
A yammacin jiya Asabar ne Trump ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta soma tsara yadda za a kai hari Nijeriya bayan da ya yi zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Amurka a shirye ta ke ta aike da sojoji da manyan makamai cikin Najeriya don bai wa Kiristocin kariya.
Barazanar shugaban na Amurka na zuwa ne kwana guda bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya ba tare da ya bayyana takamaimai inda ya samu waɗannan alƙaluma ba.
“Muddin gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya nan-take, kuma mai yiwuwa za ta shiga wannan ƙasƙantacciyar ƙasar, cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’adda masu kaifin kishin Musulunci waɗanda ke yin wannan ta’asa,” in ji Trump.