Aminiya:
2025-05-01@06:27:30 GMT

’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3

Published: 14th, March 2025 GMT

’Yan bindiga sun kai hari tare da tarwatsa mazauna ƙauyuka biyar da ke Karamar Hukumar Kachia a Jihar Kaduna.

Ƙauyukan da abin ya shafa sun haɗa da Unguwan Tauka, Unguwan Lalle, Sonudazuwa, Tsauni Dodo, da Dandauka.

Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu — Obasanjo

Wani jagoran al’umma ya tabbatar da faruwar harin, inda ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun kuma kai farmaki sansanin Fulani da ke Kubuwo, inda suka sace matasan makiyaya uku.

Sun kai harin ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 6 na yamma.

Shaidu sun bayyana cewa ’yan bindigar sun isa ƙauyukan suna harbe-harbe, lamarin da ya tilasta wa mazauna ƙauyukan tserewa.

“’Yan bindigar sun shigo suna harbi ta ko ina. Mutane suka riƙa gudu don tsira da rayukansu,” in ji wani jagora.

“Sannan sun sace matasa uku a sansanin Fulani, suka tafi da su cikin daji.”

Wani jami’in tsaro ya bayyana cewa ’yan bindigar sun tserewa wani farmaki da sojoji suka kai musu a dajin Kurutu-Azara, wanda ke iyaka da Ƙaramar Hukumar Kagarko.

Ya ce a kan hanyarsu ta tserewa ne, suka farmaki ƙauyukan da ke hanyarsu.

A yayin harin, ’yan bindigar sun ƙone mota da babur a Unguwan Tauka.

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa, “An ƙone wa wani mutum mota sabuwa da ya sayo a Kaduna. Yana kan hanyar shigowa garin ne sai ya hango ’yan bindigar.

“Nan take ya fice daga motar ya tsere, suna ganin motar suma cinna mata wuta suka ƙone motar da wani babur.”

Wani ɗan banga daga cikin ƙauyukan da aka kai wa harin ya tabbatar da cewa jami’an tsaro na ci gaba da bin sahun ’yan bindigar.

Rundunar ’yan sandan yankin ta tabbatar da harin, amma ta ce za a tuntuɓi hedikwatar ’yan sandan m Kaduna don ƙarin bayani.

Sai dai kakakin rundunar, ASP Hassan Mansur, bai samu damar yin tsokaci kan harin ba lokacin da aka nemi jin ta bakinsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa hari Ƙauyuka Ƙonewa yan bindigar sun bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya kaddamar da ayarin likitoci su tara domin kula da lafiyar maniyata aikin hajjin na wannan shekaran.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan bayan ganawar farko da ayarin da kuma shugabannin hukumar.

Ayarin likitocin ƙarƙashin jagorancin Dr. Bello Jamoh, za su gudanar da cikakken binciken lafiyar maniyata kafin tafiyar su zuwa kasa mai tsarki da zai gudana a sansanin alhazai da ke Mando, Kaduna.

Sannan kuma za su bayar da taimakon gaggawa a kasar Saudiyya tare da haɗin gwiwar Ayarin likitocin daga Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON).

Shugaban hukumar ya ce mambobin ayarin za su kasance cikin tsari na duba lafiyar mahajjata a tsawon lokacin aikin hajjin.

“Lafiya maniyata aikin hajjin tana da matuƙar muhimmanci, mun zaɓi ayarin ne bisa ƙwarewarsu, kuma muna da tabbacin za su bayar da ingantaccen kulawa ta lafiya a lokacin aikin hajjin,” In ji shi.

Shugaban ya ƙara da cewa za a gudanar da cikakken gwajin lafiya ga dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajj, musamman don gano mata masu juna biyu.

Babu sassauci ko kaɗan wajen barin mata masu juna biyu su tafi Hajj.” in ji Malam Salihu, yana mai jaddada cewa gudunmuwar da ayarin likitocin za su bada wajen tabbatar da wannan doka, na da muhimmanci don bin ƙa’idodin aikin Hajjin.

Ya ja hankalin ayarin likitocin su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa da sadaukarwa, domin tabbatar da cewa mahajjata sun samu aikin hajji mai sauƙi cikin koshin lafiya.

 

Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara