Sojojin Isra’ila: Da Gangan Muke Kashe Faladinawa A Wurin Karbar Taimakon Abinci
Published: 28th, June 2025 GMT
Wasu daga cikin jami’an sojojin HKI sun yi furuci da cewa, an ba su umarni ne da su rika bude wuta akan Fararen hula Falasdinawa da suke zuwa cibiyoyin karbar kayan agaji, suna jaddada cewa, wadanda su ka kashe din ba su yin wata barazna a gare su.
Jaridar “Haarezt” ta ‘yan sahayoniya ta buga rahoton da ya kunshi furucin sojojin nasu da su ka tabbatar da cewa; An ba su umarni ne da su rika harbin duk wanda su ka gani a kusa da cibiyoyin raba kayan abinci.
Jaridar ta kuma ce; Sojojin sun yi amfani da kowadanne irin bindigogi da su ka hada da manya wajen harbin fararen hula Falasdinawa.
Yawan Falasdinawan da su ka yi shahada a cibiyoyin raba kayan agaji sun kai 80, yayin da wani adadi mai yawa ya jikkata.
Tun farkon bude cibiyoyin agajin ne dai kungiyar Hamas ta bayyana shi da cewa; Sun zama wurin farautar Falasdinawa.
MDD ta ki shiga cikin shirin, saboda ta ce, manufarsa ita ce korar Falasdinawa daga Gaza da kuma wata manufar ta soja.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Ya kara da cewa, masana’antar abinci ta Afrika na amfani da dabarun masu samar da kayayyaki na Sin, wajen samar da kayayyaki masu inganci. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp