Aminiya:
2025-06-30@20:44:24 GMT

An kashe ubangidan Turji, Kacalla Ɗanbokolo a Zamfara

Published: 30th, June 2025 GMT

Gwamnatin Zamfara ta bayyana cewa jami’an sa-kai sun kashe wani riƙaƙƙen ɗan bindiga da ya addabi wasu yankunan jihar mai suna Kacalla Ɗanbokolo.

Mai bai wa gwamnan jihar shawara kan harkokin tsaro, Ahmad Manga wanda ya tabbatar da hakan ya bayyana kisan Ɗanbokolo a matsayin gagarumin nasara a yaƙi da matsalar tsaro.

“Ɗanbokolo mutum ne da ya fi Bello Turji fitina, ya fi Turji aikata miyagun laifuka, illa kawai shi Turji sunansa da ya karaɗe kafofin yaɗa labarai,” in ji Ahmad Manga.

“Mutanensa da aka kashe sun haura 100, saboda haka wannan gagarumar nasara ce a gare mu,” in ji Manga.

Ya bayyana cewa Kacalla Ɗanbokolo ya rasa ransa a wata arangama a ƙauyen Kurya, tsakanin jami’an sa-kai na Gwamnatin Jihar Zamfara da mayaƙan ɗan bindigar.

Bayanai sun ce Ɗanbokolo ya shafe shekaru masu yawa yana kai hare-hare yankunan Jihar Zamfara tare da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Riƙaƙƙen ɗan bindigar ya gamu da ajalinsa ne tare da wasu ɗimbin mayaƙansa a lokacin da jami’an tsaron sa-kai -— da Gwamnatin Zamfara ta samar.

Mazauna yankin na kallonsa a matsayin mutum marar imani da tausayi da ya addabi yankunansu, ta hanyar kai hare-hare da kisan mutane.

“Shi mutum ne da bai yarda da sulhu ko ta wane hali ba, hatta ɗan uwansa Bello Turji ya taɓa nuna alamun amincewa da sulhu, amma shi wannan bai taɓa nuna hakan ba”, kamar yadda wani mazaunin yankin ya bayyana wa BBC.

Wannan ne karo na biyu da jami’an tsaro ke kashe riƙaƙƙun ’yan bindiga da ake gani a matsayin iyayen gida da Bello Turji.

Ana iya tuna cewa, a watan Satumban 2024 ne jami’an sojojin Nijeriya suka kashe Halilu Sububu, wanda shi ma ubangida ne ga Bello Turji a wani kwantan ɓauna da suka yi masa tare da mayaƙansa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kacalla Ɗanbokolo

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Zazzau ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato

Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin aure da aka kashe a Jihar Filato.

Tun da farko, Hakimin Basawa, Haruna Abubakar ne, ya wakilci Sarkin lokacin da lamarin ya faru, saboda Sarkin ya yi tafiya.

Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam’iyyar APC

Sarkin, ya bayyana baƙin cikinsa bisa wannan mummunan lamari, inda ya roƙi iyalan da su ɗauki wannan a matsayin ƙaddara.

Ya yaba da yadda suka yi haƙuri kuma suka bar komai ga hukuma, ba tare da ɗaukae doka a hannunsu ba.

Sarkin ya kuma tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Kaduna na ƙoƙarin ganin an bi wa waɗanda abin ya shafa haƙƙinsu.

Ya ƙara da cewa zaman lafiya da haƙuri su ne mafita ga duk wata matsala, kuma hakan zai kawo ci gaba a tsakanin al’umma.

A yayin ziyarar, Sarkin ya samu rakiyar wasu daga cikin ’yan majalisarsa da hakimai.

Ya sake roƙon jama’a da su ci gaba da zaman lafiya tare da miƙa lamarin ga Allah.

Da yake magana a madadin iyalan garin, Mallam Muhammadu Dan Bami, ya gode wa Sarkin bisa ziyarar da ya kawo, tare da bayyana cewa mutanen garin masu bin doka da son zaman lafiya ne.

Daga ƙarshe, ya roƙi Sarkin da ya taimaka wajen ganin gwamnati ta cika alƙawarin da ta ɗauka na bi masu haƙƙinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
  • Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda, Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello Turji
  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
  • Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta da Isra’ila ta kashe
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta Isra’ila ta kashe
  • Sarkin Zazzau ya ziyarci iyalan ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato