An kashe ubangidan Turji, Kacalla Ɗanbokolo a Zamfara
Published: 30th, June 2025 GMT
Gwamnatin Zamfara ta bayyana cewa jami’an sa-kai sun kashe wani riƙaƙƙen ɗan bindiga da ya addabi wasu yankunan jihar mai suna Kacalla Ɗanbokolo.
Mai bai wa gwamnan jihar shawara kan harkokin tsaro, Ahmad Manga wanda ya tabbatar da hakan ya bayyana kisan Ɗanbokolo a matsayin gagarumin nasara a yaƙi da matsalar tsaro.
“Ɗanbokolo mutum ne da ya fi Bello Turji fitina, ya fi Turji aikata miyagun laifuka, illa kawai shi Turji sunansa da ya karaɗe kafofin yaɗa labarai,” in ji Ahmad Manga.
“Mutanensa da aka kashe sun haura 100, saboda haka wannan gagarumar nasara ce a gare mu,” in ji Manga.
Ya bayyana cewa Kacalla Ɗanbokolo ya rasa ransa a wata arangama a ƙauyen Kurya, tsakanin jami’an sa-kai na Gwamnatin Jihar Zamfara da mayaƙan ɗan bindigar.
Bayanai sun ce Ɗanbokolo ya shafe shekaru masu yawa yana kai hare-hare yankunan Jihar Zamfara tare da sace mutane domin neman kuɗin fansa.
Riƙaƙƙen ɗan bindigar ya gamu da ajalinsa ne tare da wasu ɗimbin mayaƙansa a lokacin da jami’an tsaron sa-kai -— da Gwamnatin Zamfara ta samar.
Mazauna yankin na kallonsa a matsayin mutum marar imani da tausayi da ya addabi yankunansu, ta hanyar kai hare-hare da kisan mutane.
“Shi mutum ne da bai yarda da sulhu ko ta wane hali ba, hatta ɗan uwansa Bello Turji ya taɓa nuna alamun amincewa da sulhu, amma shi wannan bai taɓa nuna hakan ba”, kamar yadda wani mazaunin yankin ya bayyana wa BBC.
Wannan ne karo na biyu da jami’an tsaro ke kashe riƙaƙƙun ’yan bindiga da ake gani a matsayin iyayen gida da Bello Turji.
Ana iya tuna cewa, a watan Satumban 2024 ne jami’an sojojin Nijeriya suka kashe Halilu Sububu, wanda shi ma ubangida ne ga Bello Turji a wani kwantan ɓauna da suka yi masa tare da mayaƙansa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kacalla Ɗanbokolo
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Zartaswa ta dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu a Nijeriya
Gwamnatin Tarayya ta yanke shawarar dakatar da ƙirƙirar sabbin manyan makarantu har na tsawon shekaru bakwai masu zuwa a duk faɗin Nijeriya.
Dakatarwar ta shafi ƙirƙirar sabbin jami’o’i, kwalejojin ilimi da kuma kwalejojin kimiyya da fasaha na tarayya kamar yadda Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) ta tabbatar.
Tinubu zai tafi ziyarar ƙasashe 3 An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a BauchiWannan mataki, a cewar Ministan Ilimi Dakta Olatunji Alausa, an ɗauke shi ne domin rage yawan makarantun da ba a amfani da su yadda ya kamata, lamarin da zai ba da damar mayar da hankali wajen gyara da inganta waɗanda ake da su yanzu.
Da yake zantawa da manema labarai bayan taron na FEC a fadar shugaban ƙasa ranar Laraba, Alausa ya bayyana cewa binciken da aka gudanar ya nuna cewa samun damar shiga jami’a a Nijeriya “ba ita ce matsala ba” a halin yanzu.
Sai dai ministan ya ce yawan kafa makarantu marasa inganci da maimaita su ne ke jawo matsaloli irin su gine-ginen da ba su dace ba, ƙarancin ma’aikata, da raguwar ɗalibai.
Ya ce “akwai wasu jami’o’in gwamnatin tarayya da ke aiki ƙasa da yadda ya dace da su, inda wasu ke da ɗalibai da ba su haura 2,000 ba. A wata jami’a ma, ma’aikata 1,200 ne ke kula da ɗalibai ƙasa da 800.
“Wannan asarar kuɗin gwamnati ne, saboda a yanzu muna da jami’o’i 199, amma ƙasa da ɗalibai 100 ne suka nemi shiga kowace ta hanyar JAMB. Har ma akwai jami’o’i 34 da babu wanda ya nema gaba ɗaya,” in ji shi.