Aminiya:
2025-11-27@22:18:11 GMT

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 a Borno

Published: 1st, July 2025 GMT

Hedikwatar Tsaron Nijeriya (DHQ) ta ce dakarun tsaro na rundunar “Operation Hadin kai” sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 yayin wata arangama a yankin Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.

Daraktan watsa labarai na hedikwatar tsaron, Manjo Janar Markus Kangye ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina

Manjo Janar Markus Kangye ya ce aikin kawar da ‘yan ta’addan da aka aiwatar ranar Litinin ya faru ne bayan rundunar ta lashi takobin kawar da sauran ‘yan Boko Haram/ISWAP da ke ɓuya a yankin Tafkin Chadi.

“Arangamar ta faru ne a lokacin wani aiki na haɗaka wanda aka shirya kuma aka aiwatar cikin dabara domin kawar da sauran ‘yan ta’addan Boko Haram/ISAWP da ke aika-aika a garuruwan da ke kan iyaka,” in ji Janar Kangye.

“Dakaraun da suka yi aiki bisa bayanan sirri sun danna cikin maɓuyar mayaƙan tsakanin Rann da Gamboru, inda suka yi ba-ta-kashi sannan suka kashe ‘yan ta’adda 10,” in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa bayan arangamar an samu makamai da yawa daga wurin, ciki har da bindigogin harbo jiragen sama.

Aikin wani ɓangare ne na dabarun karɓe iko da kudancin Tafkin Chadi da kuma hana zirga-zirgar ‘yan Boko Haram ta kan iyaka, a cewarsa.

“Ana nazari kan makaman da aka ƙwace yayin da ake ƙoƙarin gano waɗanda suka tsere da kuma sauran maɓoyar ’yan ta’adda a yankin,” in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa dakarun sojin Nijeriya, da haɗin gwiwar rundunar haɗin gwiwa ta MNJTF da kuma sauran jami’an tsaro sun zafafa ayyukansu a yankin Tafkin Chadi da sauran ɓangarori na arewacin Borno domin kakkaɓe sauran ‘yan Boko Haram a yankin

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno Operation Hadin Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza

Adadin Falasdinawan da aka kashe a yakin kisan kare dangi na Isra’ila a Gaza na iya zama mafi girma fiye da yadda aka kiyasta a baya, in ji rahoton jaridar Die Zeit ta Jamus ta mako-mako.

A bisa ga kiyasin masu binciken, tsakanin Falasdinawa 99,997 da 125,915 ne aka kashe a Gaza a cikin shekaru biyu na farko na yakin.

Masana kimiyya a Cibiyar Max Planck sun tattara bayanai daga majiyoyi da yawa kafin su bayyana kididdigar.

Baya ga alkaluman da Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta fitar, sun hada wani bincike mai zaman kansa na gida da rahotannin mace-mace da aka buga a shafukan sada zumunta.

Duk da haka, asibitoci da yawa sun daina aiki yadda ya kamata a lokacin yakin, wanda hakan ya sa hukumomi suka yi amfani da sanarwar mutuwar da iyalai suka bayar.

Misali, wadanda suka mutu a karkashin baraguzan gine-gine galibi ba a rubuta su ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru  Mafaka Ta Wucin Gagi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin November 25, 2025 An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina