Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 a Borno
Published: 1st, July 2025 GMT
Hedikwatar Tsaron Nijeriya (DHQ) ta ce dakarun tsaro na rundunar “Operation Hadin kai” sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 yayin wata arangama a yankin Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.
Daraktan watsa labarai na hedikwatar tsaron, Manjo Janar Markus Kangye ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.
Manjo Janar Markus Kangye ya ce aikin kawar da ‘yan ta’addan da aka aiwatar ranar Litinin ya faru ne bayan rundunar ta lashi takobin kawar da sauran ‘yan Boko Haram/ISWAP da ke ɓuya a yankin Tafkin Chadi.
“Arangamar ta faru ne a lokacin wani aiki na haɗaka wanda aka shirya kuma aka aiwatar cikin dabara domin kawar da sauran ‘yan ta’addan Boko Haram/ISAWP da ke aika-aika a garuruwan da ke kan iyaka,” in ji Janar Kangye.
“Dakaraun da suka yi aiki bisa bayanan sirri sun danna cikin maɓuyar mayaƙan tsakanin Rann da Gamboru, inda suka yi ba-ta-kashi sannan suka kashe ‘yan ta’adda 10,” in ji sanarwar.
Ya ƙara da cewa bayan arangamar an samu makamai da yawa daga wurin, ciki har da bindigogin harbo jiragen sama.
Aikin wani ɓangare ne na dabarun karɓe iko da kudancin Tafkin Chadi da kuma hana zirga-zirgar ‘yan Boko Haram ta kan iyaka, a cewarsa.
“Ana nazari kan makaman da aka ƙwace yayin da ake ƙoƙarin gano waɗanda suka tsere da kuma sauran maɓoyar ’yan ta’adda a yankin,” in ji sanarwar.
Ya ƙara da cewa dakarun sojin Nijeriya, da haɗin gwiwar rundunar haɗin gwiwa ta MNJTF da kuma sauran jami’an tsaro sun zafafa ayyukansu a yankin Tafkin Chadi da sauran ɓangarori na arewacin Borno domin kakkaɓe sauran ‘yan Boko Haram a yankin
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno Operation Hadin Kai
এছাড়াও পড়ুন:
Bincike Ya Tabbatar da Cewa HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 Tun Bayan Fara Yaki A Gaza
Masu bincike sun gano cewa sojojin HKI sun kashe Falasdinawa akalla 100,000 tun bayan fara yakin tufanul Aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara 2023.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kan cewa farfesa Michael Spagat da kuma Khalil Shikaki Bafalasdine masanin masanin fasahar siyasa a Jami’ar London na kasar Burtania suka jagoranci bincike wanda ya kai ga fitar da wannan sakamakon.
Labarin ya kara da cewa masu binciken sun kiyasta mutane a gidaje 2000 a birnin Gaza kadai wanda falasdinawa kimani 10,000 suke rayuwa, sannan suka yi lissafi suka kaim ga wannan sakamakon.
Bincike ya kara da cewa daga watan jenerun shekara ta 2025 falasdinawa 75,200 sojojin yahudawan suka kashe da makamai, sannan wasu kimani 8,540 sun mutu sabada yunwa da karancin magunguna da kuma wasu hanyoyi ba da wuta ba.
Amma ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta bayyana cewa daga watan Jeneru zuwa yanzu sojojin yahudawan sun kashe falasdinawa 10,000.
Ma’aikatar ta kara da cewa a baya bayan nan sojojin yahudawa suna kashe Falasdinawa a wuraren karban abinci da suka shirya a matsayin tarko ga Falasdinawa wadanda suke fama daga tsananin yunwa.