Aminiya:
2025-08-16@01:01:18 GMT

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 a Borno

Published: 1st, July 2025 GMT

Hedikwatar Tsaron Nijeriya (DHQ) ta ce dakarun tsaro na rundunar “Operation Hadin kai” sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 yayin wata arangama a yankin Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.

Daraktan watsa labarai na hedikwatar tsaron, Manjo Janar Markus Kangye ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina

Manjo Janar Markus Kangye ya ce aikin kawar da ‘yan ta’addan da aka aiwatar ranar Litinin ya faru ne bayan rundunar ta lashi takobin kawar da sauran ‘yan Boko Haram/ISWAP da ke ɓuya a yankin Tafkin Chadi.

“Arangamar ta faru ne a lokacin wani aiki na haɗaka wanda aka shirya kuma aka aiwatar cikin dabara domin kawar da sauran ‘yan ta’addan Boko Haram/ISAWP da ke aika-aika a garuruwan da ke kan iyaka,” in ji Janar Kangye.

“Dakaraun da suka yi aiki bisa bayanan sirri sun danna cikin maɓuyar mayaƙan tsakanin Rann da Gamboru, inda suka yi ba-ta-kashi sannan suka kashe ‘yan ta’adda 10,” in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa bayan arangamar an samu makamai da yawa daga wurin, ciki har da bindigogin harbo jiragen sama.

Aikin wani ɓangare ne na dabarun karɓe iko da kudancin Tafkin Chadi da kuma hana zirga-zirgar ‘yan Boko Haram ta kan iyaka, a cewarsa.

“Ana nazari kan makaman da aka ƙwace yayin da ake ƙoƙarin gano waɗanda suka tsere da kuma sauran maɓoyar ’yan ta’adda a yankin,” in ji sanarwar.

Ya ƙara da cewa dakarun sojin Nijeriya, da haɗin gwiwar rundunar haɗin gwiwa ta MNJTF da kuma sauran jami’an tsaro sun zafafa ayyukansu a yankin Tafkin Chadi da sauran ɓangarori na arewacin Borno domin kakkaɓe sauran ‘yan Boko Haram a yankin

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno Operation Hadin Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno – INEC

Hukumar Zaɓe Mai zaman kanta ta Ƙasa a Jihar Borno ta bayyana cewa, babu tabbas na gudanar da aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a na shekarar 2025/2026 a wasu Ƙananan hukumomin Jihar huɗu don matsalar tsaro.

Ƙananan hukumonin sun haɗa da: Ƙaramar Hukumar Abadam da Guzamala da Marte da Kala-Balge

Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi

Bayanin hakan dai ya fito ne daga bakin Kwamishinan zaɓe na Jihar Borno, Abubakar Ahmad Ma’aji a jawabinsa ga manema labarai a Maiduguri, a wani ɓangare na shirye-shiryen fara gudanar da aikin rijistar masu kaɗa kuri’a a ranar Litinin da ke tafe.

Kamar yadda Kwamishinan Hukumar zaɓen ke bayyanawa, INEC ta mayar da rijistar masu kaɗa ƙuri’a na ci gaba da gudana a Ƙaramar hukumar Abadam zuwa kan hanyar Baga daura da ofishin Yerwa Peace.

Haka nan shi kuma aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a na Ƙaramar hukumar Guzamala an mayar da shi a sashen kashe gobara na rukunin gidaje 1,000.

Sauran Ƙananan hukumomin kamar Ƙaramar hukumar Kala-Balge an mayar da aikin ya zuwa  makarantar firamare ta Goni Kachalari da ke birnin na Maiduguri.

Shi kuma aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a na Ƙaramar hukumar Marte an mayar da shi ya zuwa Kachamai, waɗanda dukkansu suna cikin birnin Maiduguri ne.

Don haka Kwamishinan ya yi kira ga mutanen waɗannan ƙananan hukumomin da su yi haƙuri da wannan canji da aka samu an yi ne da kyakkyawar manufar da duk wanda abin ya shafa zai samu rijistar katinsa na kaɗa ƙuri’a cikin kwanciyar hankali.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno – INEC
  • Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC
  • Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
  • Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Maku Guda – DHQ
  • Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Sojoji sun kashe babban Kwamandan ISWAP, Amirul Fiya a Borno
  • Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
  • Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin