Jagoran wannan sabuwar tafiya kuma tsohon sakataren gwamnatin Jihar Katsina, Mustapha Inuwa ne ya bayyana haka a lokacin da tsaffin ‘yan takarar suka je ofishinsa domin jadadda goyon bayansu kan sabuwar tafiya.

Shi ma da yake magana a madadin sauran ‘yan takarar majalisar dokokin jiha a zaben 2023, Hon.

Jamilu Yahaya ya bayyana cewa sun fice daga jam’iyyar PDP ne saboda yadda aka nisantar da su daga al’umma wanda su ne ke yin zabe.

A nashi bangaren, shugaban ‘yan takarar shugabancin kananan hukumomi, Hon. Yasir Ibrahim ya ce sun shiga wannan hadaka ne saboda irin yaudarar shugabanci da aka yi masu a tsohuwar jam’iyyar PDP da ke fama da rikice-rikice.

Da yake nasa tsokaci, shugaban tsaffin ‘yan takarar kansiloli na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, Hon. Usman Aminu ya bayyana cewa su 225 ne suka amince da wannan sabuwar tafiya, amma yana kokarin ganin sauran ma sun shiga an yi da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yan takarar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin Bola Tinubu da amfani da Hukumar EFCC wajen yi wa masu adawa da ita barazana.

Saƙon da ɗan takarar shugaban ƙasa a Zaɓen 2023 ya wallafa wannan Talatar a shafinsa na X, na zuwa ne bayan tsare tsohon Gwamnan Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal da EFCCn ta yi.

Amurka da China sun dakatar da harajin da suka ƙaƙaba wa juna Harin ’yan fashi: An rufe Federal Poly Bauchi Bauchi

A cewar Wazirin Adamawa, “dalilin da EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal, shi ne saboda yana cikin jam’iyyar adawa ta haɗaka.

“Wannan yana ƙara nuna yadda gwamnatin Tinubu ke ci gaba da yaɗa manufofinta na musgunawa, tsoratarwa, da rusa ‘yan adawa.”

Ya ƙara da cewa, “A yau dai duk wanda yake da alaƙa da ‘yan adawa to za a zarge shi da cin hanci da rashawa.

“Kuma da zarar an tilasta musu komawa kan tsarin tafiyar siyasar Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu, sai ya zama kamar an gafarta musu zunubansu ne.”

Martanin PDP

Ita ma jam’iyyar PDP reshen Jihar Sakkwato ta soki tsarewar da aka yi wa tsohon gwamnan, tana bayyana lamarin a matsayin “tuggun siyasa.”

Mai magana da yawun jam’iyyar a jihar, Hassan Sahabi Sanyinnawal, ya bayyana shi a matsayin yunƙurin rufe bakin jam’iyyun adawa da tsoratar da su.

Rahotanni sun ce EFCC da ke da alhakin yaƙi ta masu yi wa tattalin arziki ta’annati ta tsare Tambuwal a Abuja ranar Litinin kan zargin cire naira biliyan 189 ba bisa ƙa’ida ba, abin da ya saɓa wa dokar haramta sama-da-faɗi da kuɗi ta 2022.

Sai dai wasu majiyoyi daga hukumar sun ce gayyata ce kawai aka yi masa domin ya yi ƙarin haske kan batun, ba kama shi ba.

Tambuwal wanda ya taɓa zama shugaban Majalisar Wakilan Nijeriya, ya fara siyasarsa a jam’iyyar APC kafin ya koma PDP, sannan daga bisani ya shiga jam’iyyar haɗaka ta ADC, wacce ta ɗaura ɗamarar karɓe mulki daga hannun APC a 2027.

A bayan nan wasu rahotanni sun bayyana cewa EFCC ta gayyaci tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai kuma tsohon gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, wanda ake sa ran zai amsa cikin mako ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara
  • Wakilan Hamas sun isa a Alkahira don tattaunawa kan sabuwar shawarar tsagaita wuta a Gaza
  • Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello
  • Tinubu na amfani da EFCC ya muzguna wa ’yan adawa — Atiku
  • Ministan Harkokin Wajen Iraki Ya Bukaci Zaman Tattaunawa Tsakanin Kungiyar Larabawan Yankin Tekun Gulf Da Iraki Da Kuma Iran
  • Giyar mulki Na Jan Trump – Ƴan Democrats
  • Tinubu Ya Jinjinawa NAFDAC Bisa Matsayin Da Ta Taka A Hukumar Lafiya Ta Duniya
  • Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC
  • Mahukuntan Iraki Sun Bayyana Cewa: Akwai Yiwuwar Masu Ziyarar Arba’een Na Imam Husaini {a.s} Zasu Zarce Miliyan 4
  • Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA