Kalibof Ya Mayarwa Shugaban Kasar Amurka Martani Kan Mummunan Kalamansa
Published: 29th, June 2025 GMT
Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Muhammad Bakir Qalibof ya bayya shugaban kasar Amurka Donal Trump a matsayin mutum wanda baya iya yin magana guda ya tsaya kanta, mutumtum ne wanda yake tupka da warwara a lokaci guda.
Tashar talabijin ta Presstva a nan Tehran ta nakalto kakakin majalisar dokokin yana fadar haka a zaman majalisar dokokin kasar a jiya Talata.
Qalibof ya kara da da cewa kalaman da Trump yake fada na kaskanta shugabannin JMI yana daga cikin yakin kwakwale ne da mutanen kasar Iran. Kuma yakamata ya sani, kuma wadanda suke tare da shi su sani mutanen Iran zasu ci gaba da kare kansu su kuma yaki da wadanda suke shishigi a kan kasarsu.
Daga karshen yan siyasan makiya ne zasu bace a cikin kwandon sharer siyasa nan ba da daewa ba.
Tun lokacinda Amurka ta kai hare-haren kan cibiyoyin nukliyar kasar Iran guda uku wato Natanz ta Fordo da kuma Esfahan ne kasashen biyu suke mu sayar magangannu a tsakaninsu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘Zan iya shiga mummunan yanayi idan Dangote bai aure ni ba’
Wata ’yar siyasa a jihar Bauchi mai suna Aishatu Haruna, ta ce ta shafe shekaru shida tana dakon soyayyar attajirin nan na Afirka, Alhaji Aliko Dangote a ranta, inda ta ce za ta iya shiga mummunan hali idan bai aure ta ba.
Ta ce sau uku tana yin mafarkin ta aure shi, kuma ba ta jin za ta iya auren wani ba shi ba a duniya.
A cikin wata tattaunawarta da gidan rediyon Albarka da ke jihar Bauchi, Aishatu, wacce aka fi sani da Gimbiyar Mawakan Bauchi, ta kuma ce sau uku tana zuwa kamfanin attajijin na Obajana, ko za ta hadu da shi a can.
Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura Lafiyar Tinubu kalau – SoludoAishatu wacce a 2019 ta yi takarar neman zama Majalisar Jiha dai ta wallafa hotonta ne dauke da katin gayyatar daurin aurenta da attajirin a shafukan sada zumunta, inda ta ce tana ganin ta wannan hanyar ce sakonta zai isa gare shi.
A cewarta, “Ita soyayya a zuci take, kuma ni na gamsu shi nake so, saboda yadda yake amfani da dukiyar da Allah ya ba shi wajen hidimta wa al’umma ba iya Najeriya ba, har ma da Afirka.
“Kusan shekara shida ke nan da farawar abin. Akwai lokacin ma da na yi tattaki na tafi har kamfaninsa na siminta da ke Obajana a jihar Kogi da nufin na gan shi har sau uku, amma bai yiwu ba.
“Dalilin da ya sa na buga katin shi ne saboda na san nan ce hanya mafi sauri da zai san da ni, kuma na san babu abin da ya gagari Allah,” in ji ta.
Sai dai ta tsaya kai da fata cewa ba don dukiyarsa take son shi ba, kawai ji ta yi shi kadai ne ya kwanta mata a ransa.
“Babu wanda aka haifa da dukiya, kuma ba don ita nake son shi ba, don haka ba maganar kwarya ta bi karya don baa bin da ya gagari Allah. Ni kawai yana burge ni ne,” in ji ta.
Ta ce ta gaji da dakon soyayyar a zuciyarta, shi ya sa yanzu ta fito da ita a shafukan sada zumuntar domin kada ta shiga wani halin.