Leadership News Hausa:
2025-06-15@08:35:16 GMT

Manchester United Ta Kai Zagayen Gaba Na Gasar Europa League 

Published: 14th, March 2025 GMT

Manchester United Ta Kai Zagayen Gaba Na Gasar Europa League 

A makon da ya gabata Manchester United ta buga canjaras a wasan da Real Sociedad na gasar Europa League zagaye na farko a filin wasa na Reale Arena dake Sen Sebastian.

Amma Man Utd ɗin ta gasgata abinda bahaushe ke cewa kowa a gidansa Sarki ne bayan ta zazzagawa Sociedad ƙwallaye 4 a raga, da kuma wannan sakamakon ne United wadda Ruben Amorim ke jagoranta ta tsallaka zuwa matakin na kusa da na kusa da na karshe a gasar ta Europa League.

Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028 Bayan Shekaru 115 Manchester United Za Ta Gina Sabon Filin Wasa

Kyaftin din masu masaukin baƙin Bruno Fernandes ne ya zura ƙwallaye uku rigis a wasan kafin Diogo Dalot ya jefa ta huɗu, duk da cewar United ɗin aka fara jefa wa ƙwallo a raga amma hakan bai sa sun yi sanyin gwuiwa a Old Trafford ba.

Yanzu Manchester United za ta hadu da Olympic Lyon ta ƙasar Faransa a wasan zagayen na kusa da na ƙarshe da za a buga ranar 10 ga watan Afrilu mai kamawa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka

Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda ya tattauna ta wayar tarho da jami’ar harkokin waje ta tarayyar turai ya bayyana cewa, ci gaba da tattaunawa a tsakanin Iran da Amurka ba shi da wata ma’ana, kamata ya yi jami’an tarayyar turai din su yi Allawadai da wuce gona da irin HKI akan Iran.

Da safiyar yau Asabar ne dai jami’ar diplomasiyyar ta turai Kaja Kallas ta kira yi minsitan harkokin wajen jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci inda su ka tattauna halin da ake ciki a yammacin Asiya da ya hada da harin da HKI ta kawo wa Iran.

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana harin na HKI da cewa, wuce gona da iri ne da keta hurumin kasar Iran, kuma harin da ta kai wa cibiyoyin Nukiliya ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama da su ka hada da malaman jami’oi , da kuma mata da kananan yara.

Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su yi Allawadai da abinda HKI ta yi na take dokokin kasa da kasa.

Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Jamhuriyar musulunci ta Iran ya yi ishara da cewa, kudurin da majalisar alkalai ta hukumar makamashin Nukiliyar Iran ta fitar akan Iran wanda kuma kasashe uku na turai tare da Amurka su ka gabatar da shi, shi ne ya bude wa ‘yan Sahayoniya mashigar da su ka yi amfani da ita wajen wuce gona da iri akan Iran.

A nata gefen babbar jami’ar diplomasiyyar tarayyar turai ta bayyana rashin jin dadinta akan abinda yake faruwa a cikin yankin na yammacin Asiya na rikice-rikice, tare da bayyana cewa suna goyon bayan aiki da diplomasiyya domin tabbatar da zaman lafiya.

A wani labarin mai alaka da wannan kasar Oman ta sanar da cewa, ba za a yi taron da aka shirya yi a tsakanin Iran da Amruka ba.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Oman ce ta fitar da sanarwar cewa; Tattaunawar da aka shirya cewa za a yi a tsakanin Amurka da Iran ba za a yi ta ba a gobe Lahadi.

Ministan harkokin wajen na Oman ya kara da cewa; Diplomasiyya ce kadai ya kamata ta zama hanyar cimma zaman lafiya mai dorewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas