Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
Published: 2nd, July 2025 GMT
Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta sanar da kammala dawo da dukkan alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana gida Najeriya daga kasar Saudiyya.
A cikin wata sanarwar da Daraktar Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta fitar ranar Laraba, ta ce jirgin karshe dauke da alhazai 88 ya bar birnin Jiddah da misalin karfe 10:30 na safe dauke da alhazan jihar Kaduna da Katsina.
A cewar hukumar, hakan ya kawo karshen jigilar da aka shafe kwana 20 ana yi tun ranar 13 ga watan Yuni.
A sakonsa na bankwana ga alhazan, shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bayyana godiyarsa ga Allah kan kammala aikin cikin nasara.
Ya kuma bukaci alhazan da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’ar Allah ya kawo mata karshen tarin matsalolin da suke addabar ta.
Farfesa Abdullahi ya kuma tunatar da su cewa Aikin Hajji ibada ce da take nuna zaman lafiya da kwanciyar hankali, sannan ya buƙace su da su ci gaba da zumuncin da suka ƙulla a tsakaninsu lokacin ibadar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC
Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ce matsalar tsaro na iya hana ta gudanar da aikin rijistar masu zabe a kananan hukumomin jihar Borno guda hudu.
Kananan hukumomin da lamarin zai iya shafa su ne Abadam, Guzamala, Marte da Kala-Balge.
Jama’a ba sa yaba wa kokarinmu na hana aikata laifi – Babban Sufeton ’Yan Sanda NAJERIYA A YAU: Halin ƙuncin da ’yan fansho ke ciki a NajeriyaBayanin hakan dai ya fito ne daga bakin Kwamishinan Zabe na jihar, Abubakar Ahmad Ma’aji a jawabin sa ga manema labarai a Maiduguri, a wani vangare na shirye-shiryen fara gudanar da aikin rijistar masu kada kuri’a a ranar Litinin da ke tafe.
A cewar shi, INEC ta mayar da rijistar masu zaben a karamar hukumar Abadam zuwa kan hanyar Baga, daura da ofishin Yerwa Peace.
Kazalika, ya ce a karamar hukumar Guzamala an mayar da wurin yin rajistar sashen kashe gobara na rukunin gidaje 1,000.
Ya ce sauran kananan hukumomin kamar karamar hukumar Kala-Balge an mayar da aikin ya koma zuwa makarantar firamare ta Goni Kachalari da ke birnin Maiduguri.
Shi kuma aikin rijistar masu kada kuri’a na qaramar hukumar Marte an mayar da shi ya zuwa Kachamai, wadanda dukkansu suna cikin birnin Maiduguri ne.
Don haka kwamishinan ya yi kira ga mutanen kananan hukumomin da su yi hakuri da wannan canji da aka samu, inda ya ce an yi ne da kyakkyawar manufar da duk wanda abin ya shafa zai samu rijistarsa cikin kwanciyar hankali.