Aminiya:
2025-07-03@01:55:35 GMT

Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana

Published: 2nd, July 2025 GMT

Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta sanar da kammala dawo da dukkan  alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana gida Najeriya daga kasar Saudiyya.

A cikin wata sanarwar da Daraktar Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta fitar ranar Laraba, ta ce jirgin karshe dauke da alhazai 88 ya bar birnin Jiddah da misalin karfe 10:30 na safe dauke da alhazan jihar Kaduna da Katsina.

Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta

A cewar hukumar, hakan ya kawo karshen jigilar da aka shafe kwana 20 ana yi tun ranar 13 ga watan Yuni.

A sakonsa na bankwana ga alhazan, shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bayyana godiyarsa ga Allah kan kammala aikin cikin nasara.

Ya kuma bukaci alhazan da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’ar Allah ya kawo mata karshen tarin matsalolin da suke addabar ta.

Farfesa Abdullahi ya kuma tunatar da su cewa Aikin Hajji ibada ce da take nuna zaman lafiya da kwanciyar hankali, sannan ya buƙace su da su ci gaba da zumuncin da suka ƙulla a tsakaninsu lokacin ibadar.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

 Iran Ta Jinjina Wa Matsayar Da Pakistan Ta Dauka Akan Harin Da HKI Ta Kawo Wa Iran

Janar Abdurrahim Musawi wanda ya tattauna ta wayar tarho ta kwamandan sojojin jamhuriyar  musulunci ta Pakistan, Asim Munir, ya yi jinjina akan mataki na jarunta da Pakistan din ta dauka akan harin da HKI ta kawo wa Iran, haka nan kuma yadda ta nuna goyon bayanta ga Iran.

Janar Musawi ya  kuma yi ishara da matsayar gwamnati da al’ummar Pakistan akan ta’addanci na HKI, kamar kuma yadda ya bayyawa kwamandan sojojin kasar ta Pakistan yadda Amurka ta taimakawa HKI a tsawon kwanaki 12 na yakin.

 Har ila yau, janar Musawi ya ce; Tare da cewa mun rasa kwamandoji masu girma a farkon harin ta’addancin, sai dai kuma duk da haka, mun hana ‘yan sahayoniyar cimma manufofinsu.

A farkon yakin dai, kasar Pakistan ta bakin shugabanninta sun yi tir da harin na HKI, tare da nuna cikakken goyon bayansu ga jamhuriyar musulunci ta Iran wacce su ka bayyana a matsayin ‘yar’uwa kuma makwabciya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwalejin Koyar Da Aikin Jinya Ta Jigawa Za Ta Fara Bada Shaidar Babbar Difiloma
  • Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
  • Za mu shige gaba idan aka dawo da tattauna shirin nukiliyar Iran — EU
  • Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen VC Na Jami’ar Bayero Ta Kano 
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya
  • Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
  •  Iran Ta Jinjina Wa Matsayar Da Pakistan Ta Dauka Akan Harin Da HKI Ta Kawo Wa Iran
  • Najeriya A Yau: Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya