Tsangayar Kwalejin koyar da aikin Jinya ta Jihar Jigawa dake garin Birnin kudu ta gudanar da bikin kaddamar da sabbin dalibai 116 da za su yi karatun difloma ta kasa da babbar difloma ta kasa karon farko na shekarar karatu ta 2024 zuwa 2025.

A jawabinsa wajen taron kaddamar  da daliban,  kwamishinan ma’aikatar lafiya na jihar Jigawa Dr.

Muhammad Abdullahi Kainuwa, ya ce aikin sa na farko daga samun wannan mukami shi ne batun kafa hukumar Gudanarwar Kwalejin da sake fasalin Kwalejin, wanda hakan ya bada damar tantancewa da kuma samun amincewar Cibiyar kula da makarantun aikin Jinya ta Najeriya.

Yana mai cewar, daukar wannan mataki ya bada damar kara yawan dalibai da Kwalejin take dauka daga 120 zuwa 240, wanda hakan zai bada damar yaye dalibai masu yawa.

A cewarsa, jihar tana da ma’aikatan jinya 1,669 wanda ke nuni da gibin 1,883 in aka kwatanta da bukatar irin wadannan ma’aikata 3,552 domin kula da marasa lafiya a asibitoci.

Dr Kainuwa ya kuma taya murna ga tsangayoyin Kwalejin da ke Babura da Birnin kudu bisa kyakkyawan sakamako da suka samu a jarrabawar da ta gabata, inda su ka zamo kan gaba a tsakanin jihohin kasar nan.

Ya bayyana kiwon lafiya a matsayin kan gaba cikin kudurorin Gwamna Malam Umar Namadi guda 12, yana mai jaddada aniyar gwamnati na cigaba da bada kulawa sosai ga harkokin lafiya wanda yanzu haka ana inganta matsakaitan asibitoci 181 da kayan aiki da sauransu.

A jawabin shugaban Hukumar Gudanarwar Kwalejin Malam Salele Abdul, ya bukaci iyayen dalibai da kada su saki hannu bayan samun guraben karatu a kwalejin, domin kuwa akwai bukatar cigaba da ba su kulawa domin su kai ga nasara zuwa karshen karatunsu.

Malam Salele Abdul ya bayyana kwamishinan lafiya Dr Muhammad Kainuwa a matsayin Garkuwan Aikin Jinya bisa nasarorin da aka cimma a lokacinsa.

Kazalika, ya godewa wakilan hukumar gudanarwar da shugabannin Kwalejin bisa gudummawar da su ke bayarwa ga cigaban harkokin kealejin.

Tun da farko a jawabinsa, shugaban Kwalejin koyar da Aikin Jinya ta Jihar Jigawa, Malam Garba Adamu, wanda ya bayyana kudurinsa na ci gaba da samar da kyakkyawan yanayin koyo da koyarwa, ya kuma baiwa iyayen dalibai tabbacin horas da ‘ya’yansu kan doron Ilimi da kyakkyawar tarbiyya.

Daraktar Kwalejin Aikin Jinya Hajiya Rasheeda Musa Ya’u ta gabatar da sabbin daliban 116 maza da Mata ga Magatardar Kwalejin Malam Muhammad Sale Korau wanda ya lakana musu rantsuwar kaddamarwa.

Shima a jawabinsa, shugaban kwamatin shirye shiryen taron kuma shugaban sashen koyar da Aikin Jinya na kwalejin Malam Abubakar Garba Muhammad, ya ce bikin kaddamar da daliban na daga cikin sharuddan Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Jami’oi da Manyan Makarantu ta Kasa wato (JAMB) domin fara karatun Difloma ta kasa da Babbar Difloma ta kasa a fannin aikin jiyya.

Ya kuma godewa dukkan wadanda suka bada gudummawa wajen samun nasarar taron.

Sakataren kungiyar ma’aikatan Jiyya ta kasa reshen jihar Jigawa Comrade Nurse Kamal Ahmad ya isar da sakon shugaban kungiyar ga taron, yayin da mukaddashin shugaban sashen kula da ayyukan jiyya na ma’aikatar lafiya Nurse Aminu Isa da iyalai da abokan arzikin dalibai na daga cikin maharta taron.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Kwalejin Aikin Jinya da Aikin Jinya aikin Jinya ta Aikin Jinya ta da aikin Jinya

এছাড়াও পড়ুন:

An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji

Sojojin Guinea-Bissau sun naɗa Janar Horta Nta Na Man a matsayin sabon shugaban ƙasar na rikon kwarya, kwana ɗaya bayan sun yi juyin mulki tare da kama shugaban ƙasar, Umaro Sissico Embalo.

Sojojin dai sun kwace mulkin ne yayin da ake shirin bayyana sakamakon zaɓen kasar mai cike da takaddama.

Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi

“Na rantsar da kaina a matsayin shugaban Babban Kwamandan Soja,” in ji Janar Horta bayan ya karbi rantsuwar aiki a wani biki da aka gudanar a hedkwatar sojoji a ranar Alhamis, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na AFP ya rawaito.

Daruruwan sojoji dauke da makamai sun kasance a wurin rantsuwar.

A ranar Laraba, kwana guda bayan manyan ’yan takara biyu a zaɓen shugaban ƙasa mai cike da takaddama kowannensu ya ayyana nasara, wata ƙungiyar hafsoshin soja ta bayyana cewa ta karɓi “cikakken iko” a ƙasar.

Sojojin sun karanta sanarwa a talabijin, suna bayyana cewa sun dakatar da tsarin zaɓe “har sai an ba da sanarwa ta gaba.”

Sun kifar da Shugaba Umaro Sissoco Embalo a sabon lamari na rikice-rikicen siyasa da ke yawan faruwa a ƙasar.

Wata ƙungiyar hafsoshin sojoji ta bayyana cewa ta karɓi cikakken iko da mulkin ƙasar, kwana guda bayan manyan ’yan takara biyu, Shugaba Umaro Sissoco Embalo da Fernando Dias, kowannensu ya yi ikirarin samun nasara.

Sojojin sun bayar da umarnin dakatar da tattara sakamakon zaɓen har sai an ba da sanarwa ta gaba.

Haka kuma sun bayar da umarnin rufe dukkan iyakokin ƙasa da na sama da ruwa, tare da sanya dokar hana fita da dare.

“An yin min juyinmulki,” in ji Embalo a zantarwarsa da gidan talabijin na Faransa France24 ta wayar tarho, yana mai cewa “yanzu haka ina hedkwatar babban hafsan sojoji.”

Shugaban babbar jam’iyyar adawa ta PAIGC, Domingos Simoes Pereira, ma an kama shi, in ji Haque. “Haka kuma mun ji cewa sojoji na ƙoƙarin katse intanet. An kuma sanya dokar hana fita.”

Shugaban rundunar tsaron fadar shugaban ƙasar, Denis N’Canha, shi ne dai sojan da ke jagorantar juyin mulkin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu.
  • Real Madrid za ta yi karon-batta da Olympiacos a Gasar Zakarun Turai
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta