Tsangayar Kwalejin koyar da aikin Jinya ta Jihar Jigawa dake garin Birnin kudu ta gudanar da bikin kaddamar da sabbin dalibai 116 da za su yi karatun difloma ta kasa da babbar difloma ta kasa karon farko na shekarar karatu ta 2024 zuwa 2025.

A jawabinsa wajen taron kaddamar  da daliban,  kwamishinan ma’aikatar lafiya na jihar Jigawa Dr.

Muhammad Abdullahi Kainuwa, ya ce aikin sa na farko daga samun wannan mukami shi ne batun kafa hukumar Gudanarwar Kwalejin da sake fasalin Kwalejin, wanda hakan ya bada damar tantancewa da kuma samun amincewar Cibiyar kula da makarantun aikin Jinya ta Najeriya.

Yana mai cewar, daukar wannan mataki ya bada damar kara yawan dalibai da Kwalejin take dauka daga 120 zuwa 240, wanda hakan zai bada damar yaye dalibai masu yawa.

A cewarsa, jihar tana da ma’aikatan jinya 1,669 wanda ke nuni da gibin 1,883 in aka kwatanta da bukatar irin wadannan ma’aikata 3,552 domin kula da marasa lafiya a asibitoci.

Dr Kainuwa ya kuma taya murna ga tsangayoyin Kwalejin da ke Babura da Birnin kudu bisa kyakkyawan sakamako da suka samu a jarrabawar da ta gabata, inda su ka zamo kan gaba a tsakanin jihohin kasar nan.

Ya bayyana kiwon lafiya a matsayin kan gaba cikin kudurorin Gwamna Malam Umar Namadi guda 12, yana mai jaddada aniyar gwamnati na cigaba da bada kulawa sosai ga harkokin lafiya wanda yanzu haka ana inganta matsakaitan asibitoci 181 da kayan aiki da sauransu.

A jawabin shugaban Hukumar Gudanarwar Kwalejin Malam Salele Abdul, ya bukaci iyayen dalibai da kada su saki hannu bayan samun guraben karatu a kwalejin, domin kuwa akwai bukatar cigaba da ba su kulawa domin su kai ga nasara zuwa karshen karatunsu.

Malam Salele Abdul ya bayyana kwamishinan lafiya Dr Muhammad Kainuwa a matsayin Garkuwan Aikin Jinya bisa nasarorin da aka cimma a lokacinsa.

Kazalika, ya godewa wakilan hukumar gudanarwar da shugabannin Kwalejin bisa gudummawar da su ke bayarwa ga cigaban harkokin kealejin.

Tun da farko a jawabinsa, shugaban Kwalejin koyar da Aikin Jinya ta Jihar Jigawa, Malam Garba Adamu, wanda ya bayyana kudurinsa na ci gaba da samar da kyakkyawan yanayin koyo da koyarwa, ya kuma baiwa iyayen dalibai tabbacin horas da ‘ya’yansu kan doron Ilimi da kyakkyawar tarbiyya.

Daraktar Kwalejin Aikin Jinya Hajiya Rasheeda Musa Ya’u ta gabatar da sabbin daliban 116 maza da Mata ga Magatardar Kwalejin Malam Muhammad Sale Korau wanda ya lakana musu rantsuwar kaddamarwa.

Shima a jawabinsa, shugaban kwamatin shirye shiryen taron kuma shugaban sashen koyar da Aikin Jinya na kwalejin Malam Abubakar Garba Muhammad, ya ce bikin kaddamar da daliban na daga cikin sharuddan Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Jami’oi da Manyan Makarantu ta Kasa wato (JAMB) domin fara karatun Difloma ta kasa da Babbar Difloma ta kasa a fannin aikin jiyya.

Ya kuma godewa dukkan wadanda suka bada gudummawa wajen samun nasarar taron.

Sakataren kungiyar ma’aikatan Jiyya ta kasa reshen jihar Jigawa Comrade Nurse Kamal Ahmad ya isar da sakon shugaban kungiyar ga taron, yayin da mukaddashin shugaban sashen kula da ayyukan jiyya na ma’aikatar lafiya Nurse Aminu Isa da iyalai da abokan arzikin dalibai na daga cikin maharta taron.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Kwalejin Aikin Jinya da Aikin Jinya aikin Jinya ta Aikin Jinya ta da aikin Jinya

এছাড়াও পড়ুন:

An kama manyan shugabannin ’yan ta’addan ƙungiyar Ansaru — Ribadu

Jami’an tsaro sun kama manyan shugabannin ƙungiyar ’yan ta’adda ta Ansaru, ciki har da shugaban ƙungiyar, Mahmud Muhammad Usman wanda aka fi sani da Abu Baraa.

An daɗe ana zarginsa da kitsa hare-hare masu yawa a Najeriya.

’Yan sanda sun kama matashin da ya yi garkuwa da kansa a Ondo Majalisar dokokin Gombe ta fara duba ƙudirin ƙirƙirar sabbin gundumomi 13

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ne, ya tabbatar da kamen a wani taron manema labarai da ya gudanar a Abuja, a ranar Asabar.

Ya bayyana cewa an cafke Abu Baraa a watan Yuli bayan shafe tsawon watanni ana bin diddiginsa.

Haka kuma an kama wani shugaban ƙungiyar, mai suna Abubakar Abba.

Ribadu, ya ce wannan nasara babban ci gaba ne a yaƙi da ƙungiyar Ansaru, wacce ta ɓalle daga tsagin Boko Haram a shekarar 2012.

Duk da cewa a farko ta bayyana kanta a matsayin “ƙungiya mai tausayin jama’a” daga baya ta zama mai aikata mummunan ayyukan ta’addanci.

Ta kai wa sojoji, fararen hula da kuma gine-ginen gwamnati hare-hare.

Tsawon shekaru, ƙungiyar ta samar wa kanta maɓoya a cikin birane da kuma dazuka, musamman a kusa da yankin Kainji da ke tsakanin Jihohin Neja da Kwara har zuwa Jamhuriyar Benin.

A cewar Ribadu, Abu Baraa shi ne ke da alhakin shirya ayyukan ta’addanci a sassan Najeriya da kuma sace mutane da fashi don samun kuɗaɗen da suke amfani da su wajen aikata ta’addanci.

Mataimakinsa, Mahmud al-Nigeri wanda aka fi sani da Mallam Mahmuda, ya samu horo a ƙasar Libya tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015, inda ya ƙware wajen amfani da makamai da kuma haɗa bama-bamai.

Ribadu, ya danganta su da wasu manyan laifuka da suka haɗa da ɓalle gidan yarin Kuje a 2022, da harin da suka kai wajen haƙar ‘uranium’ a Jamhuriyar Nijar.

Har ila yau, suna da hannu a sace injiniyan Faransa Francis Collomp a 2013, da kuma sace manyan mutane kamar Alhaji Musa Umar Uba na Daura a 2019 da Sarkin Wawa na Jihar Neja.

Ribadu, ya ce wannan kamen babban nasara ce a ƙoƙarin Najeriya na kawar da ta’addanci.

Ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun samu muhimman bayanai daga hannunsu, kuma ana bincike a kansu domin kawo ƙarshen ƙungiyar.

Ya jinjina wa dakarun soja da sauran hukumomin tsaro bisa jajircewarsu, inda ya bayyana wannan babban ci gaba ne wajen rushe ƙungiyar Ansaru gaba ɗaya.

Ministan Watsa Labarai, Mohammed Idris, ya roƙi ’yan Najeriya da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani domin kawo ƙarshen ta’addanci, tare da tabbatar da tsaro da ci gaban tattalin arziƙi.

Wannan nasara na zuwa ne bayan shekara tara da kama wani tsohon shugaban Ansaru, Khalid al-Barnawi, a shekarar 2016.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Iran na Shirin fara wata muhimmiyar ziyara a Armenia da Belarus
  • An kama manyan shugabannin ’yan ta’addan ƙungiyar Ansaru — Ribadu
  • Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
  • Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar
  • UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya
  • Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil
  • ASCSN Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Nada Muhammad Dagaceri Shugaban Ma’aikata
  • Za’a Fara tattaunawar Kasa Dangane Da Talauci da Kuma Rashin Adalci A Rabin Arziki A kasar
  • Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar
  • Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse