Amurka Ta Dakatar Da Tura Makamai Zuwa Kasar Ukraine Saboda Kada A Sami Karancinsu A Gida
Published: 2nd, July 2025 GMT
Gwamnatin shugaban Donal Trump na Amurka ta bada sanarwan rage yawan wasu makaman da take aikawa kasar Ukraine.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran na nakalto majiyar Fadar Majiyar fadar white House na bayyana cewa pentagon ko ma’aikatar tsaron kasar ta bada rahoton cewa rumbun ajiyar makaman kasar yayi kasa sosai don haka akwai bukatar a dakatar da aikawa kasar Ukraine wasu makaman, kamar garkuwan kare sararin samaniya da kuma makamai masu taimaka mata wajen kare kanta.
Labarin ya nakalto Anna Kelly kakakin fadar white house na cewa an dauki wannan matakin en don sanya Amurka a gaba, duk da cewa ba zata dakatar da bawa kawayenta taimakon da ya dace ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Sabunta Filin Jiragen Sama Na Ilori Zuwa Cibiyar Jigilar Kayayyaki Ta Zamani
Gwamnatin Jihar Kwara ta ce za ta yi haɗin gwiwa da Hukumar Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN) da sauran masu ruwa da tsaki domin mayar da jihar cibiyar fitar da kayan gona da na kasuwanci.
Kwamishinan Noma da Ci gaban Karkara na jihar, Dakta Afees Abolore, ne ya bayyana haka a wani taron da Hukumar FAAN ta shirya domin sanar da shirin fara jigilar kayayyaki a Filin Jiragen Sama na Ƙasa da Ƙasa na Janar Tunde Idiagbon da ke Ilori.
A cewarsa, wannan shiri na nufin kara inganta matsayin jihar tare da ƙarfafa rawar da take takawa a harkokin kasuwanci na cikin gida da waje.
Ya jaddada cewa aikin ya yi daidai da manufofin wannan gwamnati na buɗe sababbin hanyoyin fitar da kayayyaki, bunƙasa harkokin kasuwanci, da kuma ƙara samun kuɗaɗen shiga ga masu samar da kayayyaki da ‘yan kasuwa.
Dakta Abolore ya ce jigilar kayayyakin ta jiragen zai sauƙaƙa daukarsu daga gonaki, zuwa masana’antu, da wuraren sana’o’i zuwa kasuwannin cikin gida da na ƙasashen waje, wanda hakan zai ƙara musu daraja, sarrafawa da a fannoni daban-daban.
Kwamishinan ya bayyana cewa shirin zai rage asara, ya kiyaye ingancin kayayyaki, sannan ya bunƙasa damar kasuwanci a fannin kayayyakin gona, masana’antu, da kayayyakin da aka sarrafa.
Ya nuna cewa saboda cunkoson da ake samu a tashoshin jiragen sama da na ruwa da ke Legas, garin Ilori na wata dama ta musamman wajen samun fitar da kayayyaki cikin lokaci da inganci, tare da ƙara wa jihar damar gogayya da jihohi da ma kasashen duniya.
Dakta Abolore ya yi kira ga manoma, ƙungiyoyi, masu masana’antu, masu saka jari, ƙungiyoyin sufuri, ‘yan kasuwa, masu sarrafawa, da hukumomin da ke kula da doka da tsari, da su haɗa kai wajen kara inganci, yadda ake shirya kayayyaki daidai da zamani, da amfani da fasaha domin bin ka’idojin kasuwannin ƙasashen waje.
Shi ma Manajan Filin Jirgin Sama na Janar Tunde Idiagbon, Mista Suraju Aderibigbe, ya bayyana cewa za a sabunta tsohon ginin tashar zuwa sabuwar cibiyar jigilar kaya mai amfani da fasahohi na zamani domin tabbatar da tsaro wajen sarrafa nau’ukan kayayyaki daban-daban.
Ya tabbatar da cewa wannan gyara zai ƙara bunƙasa kasuwanci, samar da ayyukan yi, da kuma ci gaban tattalin arziki a fannoni da dama a jihar.
Ali Muhammad Rabi’u