HausaTv:
2025-06-29@10:50:48 GMT

Sheikh Na’im Kasim: Muna Da Karfin Ci Gaba Da Bugawa Da Abokan Gaba

Published: 29th, June 2025 GMT

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa; Babu yadda za a yi Hizbullah ta mika makamanta a cikin wannan lokacin da yaki bai kare ba, kuma HKI  tana cigaba da keta tsagaita wutar yaki.

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya bayyana masu tunani irin wannan da rashin Sanya hankali a cikinsa.

A jawabinsa na dararen Muharram a jiya Asabar, babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma ce;  Nauyi ne da ya rataya a wuya gwamantin kasar ta takawa HKI birki akan keta tsagaita da take yi wanda take kai wa fararen hula hare-hare.”

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Babu yadda za a yi Hizbullah ta ci gaba da Sanya idanu ba tare da iyaka ba, domin mu Mabiya Imam Hussain ( a.s) kuma a kodayaushe muna bayar da taken da yake cewa; Ba Za Mu Yarda Da Kaskanci Ba.”

Har ila yau, Sheikh Na’im ya kuma ce; Duk wadanda suke cewa ana bai wa HKI uzurin ta kawo hari, su daina, domin ba ta da bukatuwa da wani uzuri da za ta fake da shi, abinda yake farwua a Falasdinu da Syria shi ne babban dalili akan hakan.:

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma ce; Isra’ila tana neman mai Rauni ne ta afka masa, wannan kuwa shi ne abinda ba zai faru da mu ba, domin mun sami tarbiyya ne  ta  rashin amincewa da kaskanci.

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce: Muna da karfin bugawa da Isra’ila, idan har ya zamana shi kadai ne zabinmu, kuma za mu yi nasara domin mun dogara ne da Allah.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: magatakardar kungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Ya ce yana matuƙar daraja lokutan da suka gudanar tare.

Ya roƙi Allah ya bai wa iyalan Dantata da Dangote, Masarautar Kano, da al’ummar jihar da ƙasar baki ɗaya haƙuri da juriyar rashin wannan babban mutum.

“Allah Ya jikan shi Ya sa Aljannatul Firdaus makomarsa,” in ji Buhari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa
  • Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari
  • Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku
  • Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
  • Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
  •  Arakci:  Idan Aka Kai Iran Bango Za Ta Fito Da Hakikanin Karfin Da Take Da Shi
  • Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’
  • Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya