Sheikh Na’im Kasim: Muna Da Karfin Ci Gaba Da Bugawa Da Abokan Gaba
Published: 29th, June 2025 GMT
Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa; Babu yadda za a yi Hizbullah ta mika makamanta a cikin wannan lokacin da yaki bai kare ba, kuma HKI tana cigaba da keta tsagaita wutar yaki.
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya bayyana masu tunani irin wannan da rashin Sanya hankali a cikinsa.
A jawabinsa na dararen Muharram a jiya Asabar, babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma ce; Nauyi ne da ya rataya a wuya gwamantin kasar ta takawa HKI birki akan keta tsagaita da take yi wanda take kai wa fararen hula hare-hare.”
Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Babu yadda za a yi Hizbullah ta ci gaba da Sanya idanu ba tare da iyaka ba, domin mu Mabiya Imam Hussain ( a.s) kuma a kodayaushe muna bayar da taken da yake cewa; Ba Za Mu Yarda Da Kaskanci Ba.”
Har ila yau, Sheikh Na’im ya kuma ce; Duk wadanda suke cewa ana bai wa HKI uzurin ta kawo hari, su daina, domin ba ta da bukatuwa da wani uzuri da za ta fake da shi, abinda yake farwua a Falasdinu da Syria shi ne babban dalili akan hakan.:
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma ce; Isra’ila tana neman mai Rauni ne ta afka masa, wannan kuwa shi ne abinda ba zai faru da mu ba, domin mun sami tarbiyya ne ta rashin amincewa da kaskanci.
Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce: Muna da karfin bugawa da Isra’ila, idan har ya zamana shi kadai ne zabinmu, kuma za mu yi nasara domin mun dogara ne da Allah.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: magatakardar kungiyar
এছাড়াও পড়ুন:
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
Sanarwar ta kara da cewa, “mun yi farin cikin ganin cewar yan wasan kungiyoyin biyu da jami’an wasan duk sun bar filin wasan ba tare da samun wani rauni ba kuma jami’an tsaro suka yi musu rakiya, kungiyar ta kara da cewa an kama wasu da dama da ake zargi da hannu a rikicin tare da mika su ga hukumomin tsaro domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.
Kungiyar ta jaddada kudirinta na tabbatar da zaman lafiya da da’a, kungiyar ta jaddada cewa za ta ci gaba da tabbatar da ingancin wasan kamar yadda hukumar NPFL da hukumar kwallon kafar Najeriya NFF ta tanada, Pillars ta kuma yi kira ga magoya bayanta da su gudanar da ayyukansu cikin lumana tare da ci gaba da ba kungiyar goyon baya, amma kuma wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta ya nuna yan wasan 3SC da aka jikkata tareda raunuka a jikinsu.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA