Atiku, wanda ya tsaya takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a 2023, ya bayyana Dantata a matsayin jarumin da ke ɗaukar kasada a harkokin kasuwanci, wanda ya ce wata muhimmiyar ɗabi’a ce ta manyan masu saka hannun jari.
Ya yaba da yadda Dantata ya sauya kasuwancin danginsu daga saye da sayarwa ta hanyar gargajiya zuwa aikin gine-gine da injiniyanci na zamani, wanda hakan ya samar da dubban ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya.
Atiku ya kuma nuna girmamawa ga Dantata bisa irin taimakon da yake yi wa jama’a cikin sirri ba tare da neman ɗaukaka ko yabo ba.
“Ya kasance mai dukiya sosai amma bai taɓa nuna girman kai ba, wannan ɗabi’a ce da ba kowa ke da ita ba,” in ji Atiku.
“Ya kasance abin koyi kuma tushen ƙarfafawa ga mutane da dama.”
Ya ƙara da cewa Dantata mutum ne mai son zaman lafiya wanda ya guji maganganun da ke kawo rabuwar kau, kuma ya jajirce wajen ƙarfafa zaman lafiya a tsakanin ‘yan Nijeriya.
Atiku ya shawarci Gwamnatin Tarayya da ta girmama Dantata ta hanyar sanya sunansa a wani muhimmin gini ko cibiyar gwamnati, domin tunawa da gudunmawarsa ga ci gaban al’umma da tattalin arziƙin ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp
উৎস: Leadership News Hausa
কীওয়ার্ড: Rasuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wasu ma’aurata da wasu mutane biyar bisa zarginsu da gudanar da ɗaurin aure ba tare da izinin iyayensu ba ko kuma bin tsarin addinin Musulunci a unguwar Nasarawa da ke cikin birnin Kano. Wadanda ake zargin sun hada da ango mai suna Aminu mai
shekaru 23 da amaryarsa Sadiya mai shekaru 22. Sauran
wadanda aka kama su ne Umar mai shekaru 24 wanda ya kasance wakilin ango; Abubakar, mai shekaru 23, wanda ya kasance waliyyin amarya; Usaina, mai shekaru 21; da kuma wasu ‘yan mata guda biyu wadanda suka kasance shaidu a yayin ɗaurin auren. Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya Rahotanni sun bayyana cewa, an ɗaura auren ne akan sadaki Naira 10,000, ba tare da amincewar iyayen ma’auratan ba. Da yake tabbatar da faruwar lamarin, mataimakin babban kwamandan hukumar ta Hisbah, Dr. Mujaheeddeen Aminuddeen, ya ce an kama wadanda ake zargin ne biyo bayan korafe-korafen da ‘yan unguwar suka kai wa hukumar. Ya bayyana cewa, matakin da wadanda ake zargin suka ɗauka ya saɓawa koyarwar addinin Musulunci da kuma dokokin aure na jihar, yana mai jaddada cewa, hukumar ta Hisbah ba za ta amince da duk wani abu da ya saɓawa tsarin addini da na shari’a a jihar Kano ba. Dr. Aminudeen ya kara da cewa, a halin yanzu wadanda aka kama suna hannun Hisbah domin ci gaba da bincike. ShareTweetSendShare MASU ALAKA

Ra'ayi Riga Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang October 13, 2025

Labarai Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista October 13, 2025

Manyan Labarai Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya October 13, 2025